2027: Na Shirya Tsaf Don Yin Aiki Tare Da Peter Obi Don Ceto Ƙasar Nan, Gwamnan Bauchi
Published: 13th, March 2025 GMT
Ya ce, muddin ‘yan siyasan Nijeriya ba su haɗa kansu waje guda ba, ƙalubalen da suke cikin ƙasar nan za su yi wuyar kawuwa. Ya ce, akwai kuma buƙatar tunƙarar matsalolin taɓarɓarewar tattalin arziki a Nijeriya.
Ya ce, tuntuɓar da suka fara da gwamnan Bauchi a matsayinsa na fitaccen ɗan siyasa a Arewa kuma shugaban ƙungiyar gwamnonin PDP ya yi ne ba wai don son zuciyarsu ba, illa sai don son da suke yi da cigaban ƙasar nan da nemi mafita.
Ya lura kan cewa akwai buƙatar a fara magance matsalolin talauci a Nijeriya kafin a tunƙari sauran matsaloli. Ya yi fatan cewa za su ci gaba da irin wannan tattaunawar domin nema wa Nijeriya mafita.
Shi kuma a jawabinsa, gwamna Bala Muhammad ya ce, tabbas akwai buƙatar ‘yan siyasa su ajiye ra’ayoyinsu su nemi yadda za su haɗa kai waje guda domin ceto Nijeriya da tabbatar da shugabanci na kwarai, sai ya ce a shirye yake ya yi aiki tare da Peter Obi.
Bala wanda ya misalta Peter Obi a matsayin jagoran ‘yan adawa a Nijeriya, “Ko ma dai menene za a ce, a shirye nake na yi aiki tare da Peter Obi, mun jingine wane wane wane wane domin nemi shugabanci na kwarai a ƙasar nan.”
Bala Mohammed ya ce lokaci ya yi da za a ajiye banbance-banbance a tunƙari haƙiƙanin zahiri tare da kawar da matsalolin da suke damun Nijeriya. Ya kuma ce, ba magana ce ake ta jam’iyya ba, illa sai don ƙasar baki daya.
Daga cikin tawagar Peter Obi akwai tsohuwar ministan kuɗi, Mrs. Nenadi Usman wadanda suka ziyarci Sarkin Bauchi Rilwanu Sulaiman Adamu bayan da suka ziyarci gwamnan.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Rashin tsaro: Gwamnan AbdulRahman Ya Gana Da Sarakuna Masu Daraja Ta Daya A Jihar Kwara
“Gwamnati ta amince da hada hannu da shugabannin al’umma na cikin gida domin tabbatar da tsaro.
“Muna gode muku kan abin da kuke yi. Amma muna bukatar Sarakuna su yi magana da mutanenmu kan kokarin da dukkanmu muke yi don kare al’ummominmu daga masu kutse.”
Gwamnan ya yi kira da a inganta hadin gwiwa a tsakanin al’umma da hukumomin tsaro domin kare rayuka da dukiyoyi.
Mataimakin Shugaban Majalisar Sarakunan Jihar Kwara, Alhaji Ibrahim Bologi II, wanda shi ne Etsu Patigi, ya yaba wa gwamnan bisa hada gwiwa da su domin tabbatar da tsaro a jihar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp