Sheikh Zakzaky: Gwagwarmayar Musulunci A Lebanon Ta Sake Jaddada Kanta
Published: 23rd, February 2025 GMT
Jagoran harkar musulunci ta Najeriya wanda ya halarci jana’izar shugaban kungiyar Hizbullah Sayyid Shahid Hassan Nasrallah a birnin Beirtu ya bayyana cewa; Yadda miliyoyin mutane su ka halarci jana’izar yana nuni da cewa, gwgawarmayar musuluncin ta sake jaddada kanta.
Sheikh Ibrahim Yakub Ibrahim El_Zakzaky ya kuma ce; Sayyid Hassan Nasrallah yana a matsayin takaitaccen hoton al’ummar musulmi ne, kuma gudanar da jana’izar da na gani yana nuni da cewa; Ruhinsa yana nan a raye cikin fagen daga.
Har ila yau jagoran ja harkar musulunci a Nigeria ya ce, abokan gaba ‘yan sahayoniya sun zaci cewa ta hanyar kisan gilla za su kawo karshen gwgawarmaya,amma abinda yake faruwa a yau, yana nuni da cewa gwgawarmaya ta kara sabunta kanta, kuma da yardar Allah wannan tafarkin zai kai ga samun nasara.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Jagora: “Yan Sahayoniya Su Saurari Ukuba Mai Tsanani
Jagoran juyin juya halin musulinci na Iran Ayatullah Sayyid Ali Khamnei ya fitar da bayani a yau juma’a da a ciki ya yi wa ‘yan sahayoniya alkawalin fuskantar ukuba mai tsanani.
Bayanin na jagora ya kunshi cewa:
Da sunan Allah Mai Rahama Mai Jin Kai
Ya Ku Al’ummar Iran Masu Girma
Da safiyar yau, ‘yan sahayoniya sun miko hannuwansu da suke jike da jini, domin tafka laifuka a cikin kasarmu. Sun kuma sake bayyana hakikanin dabi’arsu mummuna fiye da kowane lokaci a baya, su ka kai wa gidajen fararen hula hari. A dalilin haka, wannan haramtacciyar kasar ta saurari sakamako mai tsanani.
Su kuma sani cewa; Sojojin Jamhuriyar musulunci masu karfi ba za su kyale su ba da yardar Allah. A yayin wannan harin kwamandoji da dama da masana sun yi shahada.
Wannan laifin da ‘yan sahayoniya su ka tafka, ya sa sun shirya wa kansu makoma mai tsanani da daci, za su kuma ga hakan babu tantanma.
Sayyid Ali Khamnei
13/06/2025