Na Fi Ɗaukar Noma A Matsayin Sana’a Fiye Da Waƙa -Rarara
Published: 23rd, February 2025 GMT
Dauda ya kara da cewa, babu wata waka da zai yi ba tare da an bukaci ya yi ta don isar da wani sako ba. Haka zalika, Shugaba Tinubu, ba shi da wani buri na tara dukiya a halin yanzu; illa kawai dai fatan barin tarihi mai kyau a matsayinsa na Shugaban kasa, kamar yadda sauran mazan jiya; irin su Sir Ahmadu Bello da Abubakar Tafawa Balewa suka bari.
Dangane da abin da wasu ke dauka cewa, ana biyana makudan kudade; don yin wakokin da za su kawar da hankalin mutane, su sani cewa; na fi mayar da hankali a kan noma fiye da yadda nake yi wa harkar waka, dalili kuwa; ni manomi ne wanda a yanzu haka duk fadin yankin da nake, babu wani mai yin noma kamar ni.
Yanzu haka, ina noma a gona mai fadin Eka fiye da 100, sannan kuma; ina sa ran samun karin wata gonar mai girman Eka 500 da zan kara a kan wadda nake nomawa yanzu. Don haka, har Dam na sa aka yi min a cikin gonata, saboda noman rani; don haka kashi 70 na kudin shiga da nake samu yanzu, ya fito ne daga harkar noma, ba waka kamar yadda wasu ke tunani ba.
Daga karshe, mawakin ya ce; babu abin da yake jin dadi idan ya aikata, fiye da taimakon gajiyayyu, “Ina matukar jin dadi idan na taimaka wa wadanda ke bukatar taimako, domin abin da na yarda da shi shi ne, muddin ka taimaki wani; shi ma zai taimaki wani, daga karshe za a rasa wani wanda zai bukaci taimako a cikin mutane”, in ji Rarara.
কীওয়ার্ড: Waka
এছাড়াও পড়ুন:
An kashe mafarauta 10 a Adamawa
Aƙalla wasu mutum 10 mafarauta sun rasa rayukansu yayin aikin ceto a ƙauyen Kopire da ke Ƙaramar Hukumar Hong ta Jihar Adamawa.
Shugaban ƙungiyar mafarautan Nijeriya reshen Arewa maso Gabas, Shawulu Yohanna ne ya tabbatar wa Aminiya hakan a ranar Talata.
Wani abin fashewa ya kashe mutum 26 a Borno An dawo da wutar lantarki a Sifaniya da PortugalA cewarsa, ajali ya katse hanzarin mafarautan ne yayin wani arbatu da mayaƙan Boko Haram da suka yi musu kwanton ɓauna a jeji.
Ya bayyana cewa, mafarautan sun tunkari maharan ne bayan samun bayanan sirri da ke nuna cewa suna shirin kai hari.
“Abin takaicin shi yadda ake yi wa Gwamnan Borno ƙafar ungulu a ƙoƙarin da yake yi na ganin an kawo ƙarshen wannan hare-hare a yankin,” in ji shi.
Yohanna ya bayyana damuwa kan yadda mayaƙan Boko Haram ke ci gaba da ƙara ƙarfi a bayan nan da ke zama abin fargaba ga mazauna yankunan da abin ya shafa.
“Mun samu labarin cewa wani jirgi mai saukar ungulu ne yake jigilar mayaƙan daga sansaninsu zuwa wuraren da suke sheƙe ayarsu ba tare fuskantar wata tirjiya ba.
“Amma ina mai tabbatar da cewa muddin Gwamnatin Tarayya ta ɗauki mataki ta hanyar tanadar makamai na zamani, za a kawo ƙarshen waɗannan maƙiya cikin lokacin ƙanƙani.”
Ya roƙi Gwamnatin Tarayya da ta tanadar wa mafarauta da ’yan sa-kai manyan makamai na zamani domin kawo ƙarshen mayaƙan Boko Haram a yankin.
Wannan harin dai na zuwa ne ƙasa da sa’o’i 12 da wasu ’yan ta’adda suka kashe fiye da mutum 30 ciki har da mata da ƙananan yara a ƙananan hukumomin Kala Balge da Gambarou Ngala da ke jihar.