Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Mutum 9 Da Harsasai 4,264 Da Muggan Makamai A Nasarawa
Published: 9th, September 2025 GMT
“Da samun rahoton, babban jami’in ‘yansanda na yankin, ya jagoranci tawagar jami’an ‘yansanda kai tsaye zuwa wurin.
“Da suka hango jami’anmu, sai suka ajiye kayan suka tsere cikin daji. Binciken wurin ya haifar da gano makaman nan: bindigogi AK-49 guda huɗu, bindigogi AK-47 guda uku, bindiga G3 guda ɗaya, bindiga ƙarama (Sub-Machine Gun) guda ɗaya, mujallu harsasai guda goma sha ɗaya, harsasai 7.
CP Mohammed ya ƙara da cewa, a wani samame da aka yi ranar 6 ga Satumba, 2025, bisa bayanan sirri, an kama wani mutum mai suna John Paul daga Abuja a tashar motar Akwanga-Wamba yayin da yake kan hanyarsa zuwa Abuja. Da aka binciki jikinsa, an gano bindigogi biyar kirar gida, kuma wanda ake zargin ya bayyana cewa da akwai abokan harkansa. Tuni ‘yansanda suka bazama nimansu.
Haka kuma da misalin ƙarfe 3:00 na dare jami’an da ke ofishin ‘E’ Division a Shabu, cikin Lafia, sun kama manyan masu ƙera bindigogi biyu, James Philip da Alpha Philip, dukkansu maza ne daga unguwar Faferuwa, Lafia.
“Bincike ya kai ga kama manyan masu saye da sai da bindigogin da aka kirar gida , waɗanda suka haɗa da Usman Abubakar daga Shendam Road, Lafia Yakubu Danladi daga Mararaba Akunza, Lafia; Usman Kasimu wanda aka fi sani da Bobo daga Bukan Sidi, Lafia; da Abdullahi Adamu daga Bukan Sidi, Lafia.
Abubuwan da aka kwato daga hannunsu sun haɗa da: bindigogi dogaye guda 13, bindigogi ƙanana guda 10, bindiga Revolver guda ɗaya, takuba guda uku, Rigunan sanye na ƴan sanda guda uku da hulun su, injinan ƙera bindiga guda uku da kayan aiki,
Yayin da yake yabawa jajircewar jami’an sa, CP Shattima Mohammed ya tabbatar wa mazauna jihar cewa rundunar ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen kawar da miyagun mutane a Nasarawa.
Ya ce, “Ina kira ga kowa ya kasance mai lura, mai bin doka, kuma ya rika bayar da bayanai ga Rundunar yan sanda.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar
“Sauran motocin da ke cikin ayarin, ciki har da wacce ke ɗauke da shugaban majalisar, da ƙyar suka iya tsayawa wanda tsakaninsu mitoci kaɗan ne daga wurin da haɗarin ya afku,” in ji wani ganau.
Majiyoyin tsaro sun tabbatar da cewa, an garzaya da jami’an ‘yansandan da suka samu raunuka zuwa babban asibitin Gumel a sume amma daga baya sun farfaɗo.
Da yake magana kan lamarin, mataimakin shugaban majalisar, Aqeel Akilu, ya yi godiya ga Ubangiji cewa, ba a rasa rayuka ba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp