’Yan bindiga sanye da hijabi sun sace mutane 11 a Zamfara
Published: 9th, September 2025 GMT
Wasu ’yan bindiga da ake zargin sun shigo cikin al’umma sanye da hijabai sun yi garkuwa da mutane 11 ciki har da masallata guda uku a Jihar Zamfara.
Lamarin ya faru ne da safiyar ranar Lahadin da ta gabata a garin Dansadau da ke Karamar Hukumar Maru, kamar yadda rahotanni daga shafin Zagazola Makama suka tabbatar.
Makama wanda kwararren mai sharhi kan yaki da tayar da kayar baya ne ya ce ‘yan bindigar sun shiga garin ne sanye da hijabai da rigunan mata da suka yi basaja da su, inda suka yi awon gaba da mutane takwas suka tsere cikin jeji.
“Dakarun sojoji da ‘yan bijilanti sun bi sawunsu, amma ba su samu nasarar kama su ba,” in ji wata majiya.
“Daga baya an tsinto wata jaka dauke da rigunan mama da hijabai da suka yi amfani da su wajen ɓatar da kama,” a cewar majiyar.
A wani lamarin mai nasaba da wannan, wasu ‘yan bindiga sun kutsa cikin garin ‘Yarlaluka da safiyar Lahadin da ta gabata, inda suka tarwatsa wasa masallata a masallaci sannan suka yi garkuwa da mutum uku.
Daya daga cikin wadanda lamarin ya shafa, Dan Asabe Alhaji Garba, tare da wasu mutum biyu da ke tare da shi a lokacin harin.
Majiyoyi sun bayyana cewa ’yan bindigar sun shiga garin salin-alin ba tare da wata fargaba ba, abin da ke nuna yadda matsalar tsaro ke kara tabarbarewa a yankin, duk da ikirarin hukumomi na yi wa tufkar hanci.
Sai dai daga baya, jami’an tsaro sun kaddamar da bincike a yankin, inda suka cafke mutane shida da ake zargin suna da alaka da hare-haren da kuma garkuwar da aka yi, da yanzu haka ana ci gaba da titsiye su a hannun hukumomin tsaro.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Jihar Zamfara
এছাড়াও পড়ুন:
Zargin Kisan Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini — Tinubu
Shugaba Bola Tinubu ya mayar wa da Shugaban Amurka, Donald Trump martani cewa Najeriya ba ta yadda da duk wani nau’in zarafin addini.
Tinubu, ya yi wannan bayani ne bayan Trump ya sake sanya Najeriya cikin jerin ƙasashen da ake kiran “Ƙasashen da ke da Babbar Matsala wajen ’Yancin Addini.”
PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu ’yan tsagin Wike Sharrin son auren Mai Wushirya aka yi min — Mansura IsaTrump ya yi iƙirarin cewa Kiristoci a Najeriya na fuskantar barazana, amma ya sha alwashin cewa Amurka za ta kare su.
A cikin wani saƙo da ya wallafa a kafafen sada zumunta, Trump ya rubuta cewa: “Addinin Kirista yana fuskantar babbar barazana a Najeriya. Ana kashe dubban Kiristoci.”
A ranar Asabar, Tinubu ya mayar da martani ta kafar sada zumunta, inda ya ce Najeriya ƙasa ce mai dimokuraɗiyya wadda kundinta ya tabbatar da ’yancin yin addini.
“Najeriya tana da cikakken tanadi a kundinta da ya tabbatar da ’yancin yin addini,” in ji Tinubu.
“Tun daga shekarar 2023, gwamnatina na aiki tare da shugabannin Kiristoci da Musulmai don magance matsalolin tsaro da ke shafar jama’a daga kowane ɓangare da addini.”
Ya ƙara da cewa, kiran Najeriya ƙasa mai matsala wajen gudanar addini ba gaskiya ba ne.
“Za mu ci gaba da kare ’yancin kowane ɗan ƙasa na yin addininsa cikin walwala. Najeriya ba ta goyon bayan zaluncin addini ko kaɗan,” in ji Tinubu.
Ya kuma ce Najeriya za ta ci gaba da haɗa kai da Amurka da sauran ƙasashe domin inganta zaman lafiya da fahimtar juna tsakanin mabiya addinai daban-daban.