Aminiya:
2025-11-02@16:54:55 GMT

An cafke mace mai safarar wiwi da ’yan fashi 4 a Gombe

Published: 9th, September 2025 GMT

Rundunar ’yan sanda ta Jihar Gombe ta samu nasarori a yaƙi da masu aikata laifuka, inda ta kama wata mata da ake zargi da safarar miyagun ƙwayoyi.

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, DSP Buhari Abdullahi, ne ya bayyana haka cikin wata sanarwa da ya fitar.

An kama mutum biyu kan zargin yi wa ƙananan yara fyaɗe a Kebbi ’Yan bindiga da masu ɗaukar musu bayanai ba su da bambanci — Gwamnan Sakkwato

Ya ce jami’an sashen kwantar da tarzoma na Anti-Violence Squad sun kama matar mai suna Rakiya Ahmed mai shekaru 53 a unguwar Barunde, inda aka same ta da ƙunshi takwas na ganyen wiwi.

A cewarsa, an cafke matar ce bayan samun sahihan bayanan sirri daga jama’a, kuma yanzu haka ana ci gaba da bincike a kanta.

DSP Abdullahi ya kuma ce rundunar ta cafke wani mutum da ake zargin barawon Adaidaita Sahu ne, da kuma wasu matasa hudu da ake zargin ’yan fashi da makami ne.

Ya bayyana cewa, jami’an ofishin ’yan sanda na Gona sun damƙe mutumin mai suna Auwal Suleiman, mai shekaru 36, a unguwar Nassarawa tare da babur din Adaidaita Sahu da aka sace daga unguwar Wuro Biriji da ke By-pass.

Ya ƙara da cewa, wasu matasa hudu masu shekaru tsakanin 18 zuwa 22 sun shiga wani gida a Hayin Kwarin Misau da makamai, inda suka ƙwace wa mai gidan abinci, kudi da waya, kafin daga bisani rundunar ‘yan sanda ta cafke su.

DSP Buhari ya ce matasan sun amsa laifin da ake zarginsu da shi, kuma an gano wasu daga cikin kayan da suka sace.

Kwamishinan ‘Yan Sanda na Jihar Gombe, CP Bello Yahaya, ya yaba wa jami’ansa bisa jajircewarsu, tare da tabbatar da ƙudirin rundunar wajen kare rayuka da dukiyoyi a jihar.

Ya kuma buƙaci jama’a su ci gaba da bayar da sahihan bayanai domin taimaka wa jami’an tsaro wajen daƙile miyagun laifuka.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: jihar Gombe Miyagun ƙwayoyi

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

Bug da kari Tinubu ya jinjina wa Shugaban jami’ar, Farfesa Wahab Olasupo Egbewole (SAN)da ‘yan tawagarsa wajen maida hankalin da suka yi na bunkasa Jami’ar da kumna kudurinta na muradun ci gaban da ake bukata.

Shi ma anashi jawabin Shugaban Jami’ar Sarkin Katsina, Alhaji. Abdulmumin Kabir Usman, wanda Wazirin Katsina, Sanata Ibrahim Idah ya wakilta, ya nuna jin dadinsa kan irin kokarin da UNILORIN saboda bunkasar ilimi da kumasamar wuraren koyon kaaratu masu kyau da kuma suka dace.

Ya yi ma kallon ayyukan da ak kaddamar a matsayin“ irin abubuwan da ake bukatar gani ke nan”da za su taimakawa lamarin koyarwa, koyo,da kuma bincike, inda ya kara da cewa yadda Jami’ar ta maida hankalinta wajen bunkasa dabarar koyon yin abubuwa zai taimakawa dalibai su tashi da sun koyi abubuwan da zasu yi baya rayuwar da suka yi cikin aji.

A nashi jawabin mataimakin Shugaban Jami’ar, Farfesa. Egbewole ya nuna farin cikinsa da godew a Shugaban kasa Tinubu kan yadda ya amince da gaiyar da Jami’ar ta yi ma shi, da kuma taimaka mata wajen tafiyar da bunkasar abubuwan jin dadi.

“Muna nan muna sa ido saboda ci gaban samun abubwan da suke taimakawa ci gaba kwarai da gaske a kowace rana kamar yadda yace yana da amincewa da yardarm ci gaba da samun hakan’’.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna November 1, 2025 Manyan Labarai Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami November 1, 2025 Manyan Labarai Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su November 1, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
  • Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
  • Gwamna Namadi Ya Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Gwamnatin Jigawa Ta Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3
  • Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar
  • An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4m
  • An sake kama shi a cikin ’yan fashi kwana 5 da fitowa daga kurkuku
  • ‘Yansanda Sun Ceto Mutum Ɗaya, Sun Kama Mace Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Dajin Kwara 
  • Gwamnatin Gombe ta saurari ra’ayoyin jama’a kan kasafin kuɗin 2026