Harin Borno: Dole ’yan Najeriya su haɗa kai su fuskanci Boko Haram — Atiku
Published: 8th, September 2025 GMT
Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya yi Allah-wadai da sabon harin da Boko Haram suka kai a Jihar Borno, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane da dama; ciki har da sojoji.
Atiku, ya bayyana halin da ’yan Najeriya ke shiga sakamakon hare-haren ta’addanci.
Ambaliyar Ruwa: NEMA ta ceto mata 2 da jaririya a Kaduna Harin Boko Haram: Zulum ya kai ziyarar jaje garin DarajamalA cikin saƙon da ya wallafa a shafukansa na sada zumunta, Atiku ya yi kira ga ’yan Najeriya da su haɗa kai wajen yaƙi da matsalar tsaro ta hanyar haɗin kan al’umma.
Ya miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan waɗanda suka rasa rayukansu, jama’ar Jihar Borno, da kuma Gwamna Babagana Umara Zulum.
Ya kuma yaba wa gwamnan bisa ziyarar jaje da ya kai wa al’ummar da abin ya shafa.
Atiku ya yi addu’ar Allah Ya gafarta wa waɗanda suka rasu, Ya kuma sanya su a Aljanna Firdausi.
Hakazalika, ya yi kira ga ’yan Najeriya da su ci gaba da jajircewa wajen samar da zaman lafiya da tsaro.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Boko Haram hari Tsaro yan Najeriya
এছাড়াও পড়ুন:
NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
Ambaliyar ruwa na cigaba da salwantar da dukiyoyi da rayukan al’ummomi da dama a sassa daban-daban na Najeriya.
Ko a farkon makon nan, hukumomi sun yi gargadin cewa akwai yiwuwar samun ambaliyar a jihohi akalla 11.
Sai dai wasu alummomin tuni suka dauki matakai don rage barnar da ambaliyar ka iya yi musu.
NAJERIYA A YAU: Masu Nau’in Jinin AS Sun Fi Masu Nau’in AA Lafiya DAGA LARABA: Dalilan Da Suka Sa Nayi Yunkurin Kashe Kaina Har Sau UkuA kan wadannan matakai shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari.
Domin sauke shirin, latsa nan