Duk Da Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ana Ci Gaba Da Kai Hare-hare Wasu Yankunan Zamfara
Published: 6th, September 2025 GMT
“Haka nan, ‘yan bindigan, suna sake kawo wani harin a wannan gari namu na Galadi da misalign karfe 10:15 na daren ranar Laraba, inda suka kewaye baki-dayan Galadin; illa bangare guda shi ma saboda gulbi ya tare wannan gefen ne, inda suka bude wa Galadin wuta ta kowane gefe baki-daya,” in ji shi.
Kazalika ya kara da cewa, “Babu shakka, wannan hari ya yi sanadiyyar asarar rayukan mutane biyar, inda kuma wasu hudu ke kwance a gadon asibiti.
“Duk da cewa, a nan muna da jami’an tsaro; amma a lokacin da suka kawo wannan hari, sai da suka mamaye sansanin jami’an tsaron baki-daya,” kamar yadda ya bayyana.
Har wa yau, wannan Bawan Allah da ke wannan yanki na Galadi da ya nemi a sakaya sunansa ya kara da cewa; wadannan hare-hare na ci gaba da afkuwa, duk kuwa da shirin da al’ummomin yankin ke yi da kuma na gwamnatin tarayya, na tattaunawar sulhu da ‘yan bindigan.
Yayin da aka tuntubi babban mataimaki na musamman ga Gwamnan Jihar Zamfara kan kafafen yada labarai, Mustafa Jafaru Kaura cewa ya yi; har yanzu matsayin gwamnatin jihar bai sauya ba game da kaucewa tattaunawa ko yin sulhu da ‘yan bindiga.
“Saboda haka, koda wani abu ya faru a wannan gari na Galadi, ko shakka babu, Gwamnatin Jihar Zamfara na matukar bakin ciki da faruwar al’amari, sannan kuma tana yin iya kokarinta wajen ganin an ci gaba da fatattakar wadannan barayi, don ganin Allah ya kawo mana saukin al’amarin.”
Bugu da kari, masana harkokin tsaro na ci gaba da yin tsokacin cewa; kokarin magance matsalar ta tsaro a yankin Arewa Maso Yammacin Nijeriya , abu ne da ke bukatar matakai irin na bai- daya.
Sannan kuma, wajibi ne a wadanda za a dauka a dauke su a lokaci guda, idan dai har ana so a ga karshen wannan matsala da ta ki ci ta ki cinyewa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4m
Rundunar ’yan sandan Jihar Borno ta raba zunzurutun kuɗi naira miliyan 63.4 ga iyalan jami’anta 84 da suka rasa rayukansu a bakin aiki.
Rundunar ta raba kudin ne a ƙarƙashin tsarin inshorar rayuwa da kuma tsarin kula da lafiyar iyali na Sufeto Janar na ’yan sanda.
An gudanar da rabon kuɗin ne a ranar Alhamis a Maiduguri babban birnin jihar kamar yadda Kakakin rundunar a jihar, ASP Nahum Kenneth Daso, ya bayyana a cikin wata sanarwa.
A cewar sanarwar, Kwamishinan ‘yan sanda na jihar, CP Naziru Abdulmajid, wanda ya wakilci Sufeto Janar na ‘yan sanda, IGP Kayode Egbetokun, shi ne ya gabatar da takardun cakin kudin ga iyalan waɗanda suka ci gajiyar tallafin.
“Harkokin da suka shafi jami’anmu da iyalansu ya kasance babban fifiko ga rundunar,” in ji CP Abdulmajid yayin taron.
Ya ce wannan shiri na nuna tausayi da rikon amana, da kuma jagoranci mai nagarta daga Sufeto Janar wajen girmama jaruman da suka sadaukar da rayukansu domin tabbatar da zaman lafiya da tsaron ƙasa.
Kwamishinan ya kuma yi kira ga iyalan da suka amfana da tallafin da su yi amfani da kuɗaɗen yadda ya dace, musamman wajen tallafa wa ilimi, kiwon lafiya, da jin daɗin rayuwar iyalansu gaba ɗaya.
Ya yaba wa Sufeto Janar bisa ci gaba da tsare-tsaren jin daɗin jami’an rundunar, yana mai bayyana su a matsayin muhimman hanyoyin da ke samar da agaji da kwanciyar hankali ga iyalan waɗanda suka rasa masoyansu.
A nata jawabin a madadin iyalan da suka amfana, Misis Nana Goni ta nuna godiya ga Sufeto Janar bisa goyon bayan da ya bayar, tana mai tabbatar da cewa za su yi amfani da kuɗaɗen yadda ya kamata don inganta rayuwar iyalansu.
Rundunar ta bayyana cewa wannan rabon tallafi ya sake tabbatar da jajircewarta wajen kula da walwala da mutuncin jami’anta da iyalansu, musamman waɗanda suka sadaukar da rayukansu wajen kare al’umma.