Aminiya:
2025-11-02@06:36:48 GMT

Mauludi: ’Yan sanda sun haramta hawa babur da daddare a Gombe

Published: 5th, September 2025 GMT

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Gombe, ta sake jaddada haramcin hawa babura daga ƙarfe 7 na dare zuwa 6 na safe, a wani mataki na tsaurara tsaro yayin bikin Mauludi a jihar.

Kakakin rundunar, DSP Buhari Abdullahi, ya ce Kwamishinan ’Yan Sandan jihar, CP Bello Yahaya, ya bayyana cewa dokar na da muhimmanci domin hana aikata laifuka musamman a lokutan bukukuwa.

An kama mace ɗauke da bindiga da N2m a otal Gwamnatin Yobe za ta ɗauki nauyin jinyar Malam Nata’ala

Ya ce an baza jami’an tsaro a wuraren taro, wuraren Mauludi da sauran wurare.

Kwamishinan ya gargaɗi jama’a da cewa dokar hana ɗaukar makamai tana nan daram, kuma duk wanda aka kama da su zai fuskanci hukunci.

Ya kuma ce ba za a lamunci tashin hankali ko karya doka ba.

Haka kuma rundunar ta roƙi shugabannin addini, masu shirya bukukuwa da sauran masu ruwa da tsaki da su kula da mabiyansu tare da yin aiki tare da jami’an tsaro.

Ta kuma buƙaci jama’a da su kai rahoton duk wani abu ko mutum da suke zargi, tare da gujewa duk wani abu da zai iya haifar da rikici.

Sannan rundunar ta yi fatan Musulmi za su gudanar da bikin Mauludi cikin kwanciyar hankali.

Hakazalika, ta tabbatar da cewa za ta ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin jama’a a jihar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Hana Hawa Babura Tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

Karamar Hukumar Gwarzo Ta Karfafa Yaƙi Da Miyagun Kwayoyi Da Shan Magani Ba Bisa Ka’ida Ba

Shugaban karamar hukumar Gwarzo, Dr. Mani Tsoho, ya yi gargaɗi ga mazauna yankin kan mummunan ɗabi’ar shan magani ba tare da shawarar likita ba, yana mai bayyana hakan a matsayin babban haɗari ga lafiya da ka iya janyo matsalolin da ke barazana ga rai.

Dr. Tsoho ya yi wannan gargaɗi ne yayin da yake ziyarar duba asibitin Gwarzo General Hospital, inda ya gana da marasa lafiya, ya duba yadda ake gudanar da ayyuka, tare da yabawa ma’aikatan lafiya bisa jajircewarsu wajen kula da jama’a.

Ya nuna damuwa cewa, yawancin matsalolin lafiya da ake fuskanta a cikin al’umma na faruwa ne sakamakon amfani ko wuce gona da iri wajen shan magunguna ba tare da shawarwarin ƙwararru ba.

Ya shawarci jama’a da su nemi shawarar likitoci da masu magunguna kafin su sha kowanne irin magani.

Shugaban karamar hukumar ya yi kira ga mazauna yankin da su rika ziyarar asibiti mafi kusa da zarar sun ji wata alamar rashin lafiya don samun kulawa cikin lokaci.

Ya tabbatar da cewa akwai likitoci da nas-nas ƙwararru a cibiyoyin lafiya na yankin da za su samar da ingantacciya kulawa.

Yayin da yake jaddada kudirin gwamnatinsa na inganta harkokin lafiya a dukkan yankuna, Dr. Tsoho ya ce hukumar tana aiki don samar da isassun magunguna, kayan aiki na zamani da kuma horaswa ga ma’aikatan lafiya.

Baya ga batun lafiya, shugaban ya kuma yi kira ga jama’a da su kasance masu lura da tsaro, tare da yin gaggawar kai rahoton duk wani motsi ko mutum da ba su yarda da shi ba ga jami’an tsaro domin daukar mataki cikin lokaci.

 

Daga Khadijah Aliyu

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Namadi Ya Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Gwamnatin Jigawa Ta Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar
  • Matsalar Talauci Da Rashin Tsawon Rai Da ‘Yan Nijeriya Ke Fuskanta
  • Matsalar Tsaro: Ko Sabbin Shugabannin Rundunar Soji Za Su Kawo Sauyi?
  • Borno ta fara fitar da kayan robobi zuwa ƙasashen waje – Zulum
  • Gwamnatin Gombe ta saurari ra’ayoyin jama’a kan kasafin kuɗin 2026
  • Karamar Hukumar Gwarzo Ta Karfafa Yaƙi Da Miyagun Kwayoyi Da Shan Magani Ba Bisa Ka’ida Ba
  • Sojoji Sun Ceto Wani Mutum Da Aka Sace A Taraba