Mauludi: ’Yan sanda sun haramta hawa babur da daddare a Gombe
Published: 5th, September 2025 GMT
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Gombe, ta sake jaddada haramcin hawa babura daga ƙarfe 7 na dare zuwa 6 na safe, a wani mataki na tsaurara tsaro yayin bikin Mauludi a jihar.
Kakakin rundunar, DSP Buhari Abdullahi, ya ce Kwamishinan ’Yan Sandan jihar, CP Bello Yahaya, ya bayyana cewa dokar na da muhimmanci domin hana aikata laifuka musamman a lokutan bukukuwa.
Ya ce an baza jami’an tsaro a wuraren taro, wuraren Mauludi da sauran wurare.
Kwamishinan ya gargaɗi jama’a da cewa dokar hana ɗaukar makamai tana nan daram, kuma duk wanda aka kama da su zai fuskanci hukunci.
Ya kuma ce ba za a lamunci tashin hankali ko karya doka ba.
Haka kuma rundunar ta roƙi shugabannin addini, masu shirya bukukuwa da sauran masu ruwa da tsaki da su kula da mabiyansu tare da yin aiki tare da jami’an tsaro.
Ta kuma buƙaci jama’a da su kai rahoton duk wani abu ko mutum da suke zargi, tare da gujewa duk wani abu da zai iya haifar da rikici.
Sannan rundunar ta yi fatan Musulmi za su gudanar da bikin Mauludi cikin kwanciyar hankali.
Hakazalika, ta tabbatar da cewa za ta ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin jama’a a jihar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda Hana Hawa Babura Tsaro
এছাড়াও পড়ুন:
‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja
Ya ce ya sayi layin wayar ne daga hannun wani Audu, ɗan kungiyar Vikings wanda ya tsere yanzu.
A wani lamari kuma, ‘yansanda sun kama wasu mutum huɗu da suka shiga gonar wani mutum a Lapai Gwari, inda suka saci kifi da darajar kuɗinsu ta kai Naira 750,000.
Babban wanda ake zargi, Hussaini Garba, ya amsa laifi tare da bayyana Ahmed Yusuf, Ibrahim Musa da Abdulazeez Bawa a matsayin mutanen da suke sayen kifin idan ya sato.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp