Leadership News Hausa:
2025-09-17@21:51:40 GMT

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Katsina

Published: 5th, September 2025 GMT

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Katsina

Karamar karamar hukumar Jibiya ita ce ta fara shirya taro domin yin sulhu da ‘yan bindigar, sai dai kuma ba a ga wakilin gwamnatin Jihar Katsina a wannan sulhu ba, amma dai an ga shugaban karamar hukumar da sauran jami’an tsaro da ake zargin daga Abuja suke halartar irin wannan taro.

An yi wannan sulhu a karamar hukumar Jibiya kimanin wata hudu da suka gabata, kuma al’amurra na ci gaba da tafiya yadda ake so, zuwa yanzu dai al’ummomi a wannan karamar hukumar na ci gaba da harkokinsu kamar ba a yi tashin hankalin ‘yan bindiga ba.

Kar a manta duk lokacin da aka yi irin wannan taro gwamnatin Jihar Katsina na cewa babu hannunta kuma ba da ita aka yi sulhu ba, amma dai maganar jama’a na jin ta ne kamar abin nan ake cewa ihu bayan hari.

Karamar hukuma ta biyu da ita ma ta shiga sulhu da barayin daji ita ce, karamar hukumar Batsari, wanda ta sha fama da hare-haren ‘yan bindiga kamar ba gobe, an yi asarar rayuka da duniyoyi, amma yanzu sakamakon wannan zaman sulhu da aka shirya tsakanin al’ummomi da ‘yan bindigar abin ya yi sauki sosai.

Kwamishinan harkokin tsaro na cikin gida, Hon. Nasiru Mu’azu Danmusa a kullum yana fada wa ‘yan jarida cewa babu ruwan gwamnatin Jihar Katsina da wancan sulhu, shi ne ya tabbatar da cewa idan aka je babbar asibitin Batsari za a ga ‘yan bindiga suna kwanshe suna karbar magani sakamakon cututtukan da suka dame su.

Ita ma karamar hukumar Danmusa ta sha fama da matsalar ‘yan bindiga sakamakon dukkan su suna makwabtaka da babban dajin Rugu da ke da iyaka da Jihar Zamfara, an yi dauki ba dadi a wannan karamar hukuma da barayin daji da al’umma da kuma jami’an tsaro.

Yanzu wadannan kananan hukumomi guda uku da aka ambata sun samu salama sun fara dawowa cikin hayyacin su, inda a yanzu kasuwanni suna cikar farin dango an fara tafiye-tafiye da daddare duk da cewa ana samun kai hare-hare jefi-jefi.

Wannan batun sulhu har gobe yana ci gaba da dore kan masana, musamman wadanda suke da ra’ayin cewa ka da a yi sulhu da barayin daji kuma suke goyon bayan matsayar gwamnatin Radda.

Babban abin da ke dore kan masana da sauran al’umma shi ne, irin yadda gwamnati ke tinkaho da zaman lafiyar da aka samu a wadannan kananan hukumomi duk da ta cewa ba ruwan ta da wannan sulhu, wani lokaci har ikirarin cewa duk wanda ya saba alkawarin da aka yi da shi ba za ta kyale shi ba.

Rahotanni sun bayyana cewa duk wuraren da aka shirya wannan zaman sulhu bana an yi noma sosai, daman barayin daji ne suka hana noman a wadannan yankuna.

Da yawa daga cikin manoma da ‘yan kasuwa da direbobin da aka tattauna da su sun bayyana cewa lallai zaman lafiya na dawowa sannu a hankali duk da cewa wani lokaci ana da fargabar dawowa wannan hare-hare.

Yanzu dai abubuwan da suka bayyana shi ne, sakamakon wannan yarjejeniya da aka kulla da al’ummomi da barayin daji ana samun saukin kai hare-haren ‘yan bindiga, sai dai ba wai an daina kai harin bane baki daya ba, ana samun rahotanni kai hare-haren ‘yan bindiga jefi-jefi.

Masana da masu sharhi kan harkokin tsaro na jin tsoron wannan sulhu da aka ce al’umma ce da kanta ta shirya ba hannun gwamanti a ciki, daga cikin abubuwan da masana ke fargaba shi ne, barayin daji suna rike da makamansu, kuma ba a bayyane cewa an ba su kudi ba, me zai faru idan suna bukatar kudaden kashewa idan bukata ta taso masu?

Abin jira a gani shi ne, yadda wannan yarjejeniya za ta ci gaba da haifar da da mai ido ko akasin haka. Allah ya kyauta.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: da barayin daji karamar hukumar wannan sulhu yan bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025

Gwamnatin Jihar Jigawa  ta amince da ƙarin kasafin kuɗi na Naira Biliyan 75 na shekarar 2025, ga gwamnatin jiha da kuma ƙananan hukumomi 27.

Kwamishinan Yaɗa Labarai, Matasa, Wasanni da Al’adu na jihar, Alhaji Sagir Musa Ahmed ne ya bayyana haka jim kaɗan bayan zaman majalisar da aka gudanar a gidan gwamnati dake Dutse, babban birnin jihar.

Ya bayyana cewa, wannan ƙarin kasafin kuɗi ya samo asali ne daga ƙarin kuɗaɗen shiga domin biyan buƙatun kuɗaɗen da suka taso, da kuma ƙarfafa manyan fannoni da za su kawo ci gaba mai ɗorewa a faɗin jihar.

Alhaji Sagir Musa Ahmed ya ce, majalisar ta amince da Naira Biliyan 58 ga gwamnatin jiha da kuma Naira Biliyan 17 ga Kananan Hukumomi 27, wanda ya shafi kashe-kashen kudade na yau da kullum da kuma manyan ayyuka.

Ya ce, wannan ƙarin kasafin kuɗin zai inganta ayyuka da tsare-tsare da ake gudanarwa a muhimman fannoni irin su ilimi, kiwon lafiya, ababen more rayuwa, noma da sauran muhimman ayyukan ci gaba.

Sagir ya ƙara da cewa, za a mika ƙarin kasafin kuɗin ga Majalisar Dokokin Jihar domin tattaunawa da amincewa da shi, kamar yadda kundin tsarin mulki da ka’idojin kasafi suka tanada.

Kwamishinan ya ƙara jaddada cewa, wannan mataki ya nuna jajircewar gwamnatin jihar wajen gudanar da mulki bisa gaskiya da adalci, da kula da kuɗaɗen jama’a yadda ya dace, da kuma tabbatar da samar da ingantattun ayyuka ga al’ummar jihar baki ɗaya.

 

Usman Muhammad Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu bai shirya gudanar da sahihin zaɓe ba a 2027 – Buba Galadima
  • Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025
  • ‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara
  • ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 40 a masallaci a Zamfara
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara
  • Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara 
  • Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi
  • Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato
  • Gwamnatin Sudan Ta Ce: Babu Sulhu Da ‘Yan Tawayen Kasar Na Kungiyar Rapid Support Forces