Wanda aka kama sunansa iro Garba mai shekaru 25 daga Zangwaye Fulani a ƙaramar hukumar Ajingi a Jihar Kano.

Ya amsa cewa shi da wasu mutane huɗu sun yi garkuwa da mutane a Kano, Jigawa da Bauchi.

An kuma samu rigunan sojoji guda uku a hannunsa.

Kwamishinan ya ce ana ci gaba da ƙoƙarin kama sauran mutane huɗun da ake zargi da hannu a garkuwar da ta faru a Sumaila, da ke Jihar Kano.

A wani lamari kuma, ’yansanda sun kama mutane huɗu da ake zargi da fasa shago a ƙaramar hukumar Malam Madori.

Waɗanda aka kama sun haɗa da: Nuhu Yusif Saleh (19), Hassan Ibrahim (19), da Nura Musa (22).

An ƙwato akwati mai ɗauke da kuɗi Naira 870,000, abun cajin waya guda biyu, na’urar PoS, wayoyi guda 20, da lasifiƙa daga hannunsu.

Jimillar mutanen da aka kama a cikin watanni biyu sun kai 156 bisa laifuka daban-daban, ciki har da safarar makamai, fashi da makami, kisan kai, fyaɗe, lalata kayan gwamnati, fataucin miyagun ƙwayoyi da sata.

Kayan da aka ƙwato sun haɗa da bindiga AK-47 guda biyu, motoci guda uku, adaidaita sahu guda ɗaya, wayoyi guda 23, shanun sata guda 14, da kuma miyagun ƙwayoyi kamar tramadol, diazepam, exol, tabar wiwi, da sauransu.

CP Muhammad ya tabbatar da cewa rundunar za ta ci gaba da yaƙi da laifuka da kuma safarar miyagun ƙwayoyi a faɗin Jihar Jigawa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Yansanda Garkuwa Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Kano Ta Inganta Cibiyoyin Horas Da Sana’o’i Domin Dakile Aikata Laifuka Tsakanin Matasa

Gwamnatin Kano ta raba kayayyakin aiki na zamani na kimanin Naira Miliyan 250  ga cibiyoyin horas da sana’o’in hannu biyu da ke Kofar Mata da Gwale, domin yaƙi da shan miyagun kwayoyi da aikata laifuffuka a tsakanin matasa, ta hanyar samar da aikin yi.

Kwamishinan Kimiyya da Fasaha, Dakta Yusuf Kofarmata, ya ce an amince da tallafin ne bisa umarnin Gwamna Abba Kabir Yusuf don bunƙasa tsare-tsaren ƙarfafa matasa a jihar.

Ya bayyana cewa an samar da injinan sarrafa fata guda 26 domin cibiyoyin wadanda al’ummar yankunan suka kafa, amma ba su da isassun kayayyakin aiki.

Ya ce Gwamna Yusuf ne ya gina Cibiyar Horaswar ta Gwale  kasancewar nan ce mazabarsa, yayin da Dakta Yakubu Adam ya taka rawa wajen gina ta Kofar-Mata.

Ya ce cibiyoyin za su samar da daruruwan ayyukan yi tare da rage matsalolin zaman kashe-wando da ta’addanci a tsakanin matasa.

 

A nasa jawabin, Ali Musa Kofar-Mata na ƙungiyar IKMA ya gode wa gwamnati bisa wannan gudummawar da ya kira mai sauya rayuwa.

Ya ce cibiyar ta fara ɗaukar matasa maza da mata, kuma horon zai ɗauki watanni uku kafin a shiga sabon zagaye.

 

Abdullahi Jalaluddeen 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
  • Gwamnatin Kano Ta Inganta Cibiyoyin Horas Da Sana’o’i Domin Dakile Aikata Laifuka Tsakanin Matasa
  • Saudiyya ta saki ’yan Najeriya 3 da ta kama kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi
  • ‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Ta Kama Bisa Kuskuren Safarar Ƙwayoyi
  • NDLEA ta kama ɗan Indiya da ƙwaya ta Naira biliyan 3 a Legas
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara
  • An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar
  • An kama mabaraci da kuɗaɗen ƙasar waje a Ilorin