Aminiya:
2025-09-17@21:50:12 GMT

Boko Haram ba kiristoci kaɗai suke kashewa a Arewa Maso Gabas — Ndume

Published: 3rd, September 2025 GMT

Sanata Ali Ndume, wanda ke wakiltar Borno ta Kudu, ya ce ba daidai ba ne a riƙa cewa Boko Haram Kiristoci kawai suke kashewa a Arewa maso Gabas.

Ya bayyana cewa ƙungiyar tana kai wa Musulmi da Kiristoci hare-hare baki ɗaya, don haka bai kamata a alaƙanta ta da addini ɗaya ba.

Kotu ta ɗaure wani mutum kan kashe saurayin ’yarsa a Ekiti An ƙone ‘ɓarawon’ babur ƙurmus a Binuwai

Ndume, ya mayar da martani ne kan wani rahoto da wata kafar yaɗa labarai ta wallafa wanda ta yi iƙirarin cewa dukkanin waɗanda aka kashe kwanan nan a hare-haren Boko Haram Kiristoci ne.

Ya ce a hare-haren da suka faru a ƙarshen mako a Jihar Borno, Musulmi biyar aka kashe a ƙauyen Ngoshe da ke Ƙaramar Hukumar Gwoza a ranar Asabar.

Sannan an kashe Kiristoci uku a ƙauyen Mussa na Karamar Hukumar Askira-Uba a ranar Lahadi.

Sanatan ya yi gargaɗin cewa yaɗa irin wannan labari yana da hatsari domin yana iya raba kan jama’a, yana rage wa sojojin da ke yaƙi da ta’addanci ƙwarin guiwa, kuma ya iya kawo mummunan sakamako.

Ya ce Boko Haram ba sa kallon addini ko ƙabila, domin kai wa talakawa hare-harensu, waɗanda kawai suke neman zaman lafiya da yin noma.

Ndume ya yaba wa sojoji bisa jajircewarsu wajen yaƙi da ’yan ta’addan, amma ya buƙaci Gwamnatin Tarayya ta ƙara kula da walwalar sojojin tare da samar musu da isassun makamai domin su samu damar yaƙar Boko Haram.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Boko Haram

এছাড়াও পড়ুন:

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

KADA ta yi gargaɗi cewa haƙurin jama’a ya ƙare, tana mai jaddada cewa shiru da halin ko-in-kula daga shugabanni ba za a ƙara yarda da shi ba. Sun yi kira da a tabbatar da adalci da kuma mayar da zaman lafiya a yankin, tare da nuna goyon baya ga iyalan mamacin da ɗaukacin al’ummar Garga.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Kano Ta Inganta Cibiyoyin Horas Da Sana’o’i Domin Dakile Aikata Laifuka Tsakanin Matasa
  • Tinubu bai shirya gudanar da sahihin zaɓe ba a 2027 – Buba Galadima
  • Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
  • ’Yan ‘Mafiya’ na ƙoƙarin kashe matatar man fetur da na gina —Ɗangote
  • Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 
  • An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar
  • Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato
  • Dole sai mun tantance wa’azi kafin a yi —Gwamnan Neja
  • Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago
  • Mutuwar majinyata: Asibitin Aminu Kano na roƙon KEDCO ya dawo da wutar lantarki