Da ina da iko da cikin mako biyu zan magance matsalar tsaron Zamfara – Gwamna
Published: 3rd, September 2025 GMT
Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya ce da a ce yana da cikakken iko da jami’an tsaro, da zai iya magance matsalar tsaron da ta addabi jihar shi a cikin mako biyu.
Gwamnan ya kuma ce ya san dukkan inda ’yan bindigar jihar suke buya.
Da yake jawabi a cikin wani bidiyo da ya karade shafukan sada zumunta, gwamnan ya ce babban kalubalen shi a yaki da ’yan bindiga a jihar shi ne rashin cikakken iko da jami’an tsaro.
ya ce shugabannin rundunonin tsaron da ke jihar suna karbar umarni ne kawai daga hedkwatocinsu da ke Abuja, bad aga wajen shi ba.
A cewar Gwamnan, “Na rantse da Allah na san duk inda wani shugaban ’yan bindiga yake a Zamfara, kuma duk inda ya fita ya je na sani.
“Yanzu da wayata zan iya nuna muku inda wadannan ’yan ta’addan suke a yau. Amma babu abin da za mu iya yi musu.
“Wallahi a yau da ina da iko da jami’an tsaro, ina mai tabbatar maka za mu iya kawo karshen ’yan bindiga a Zamfara cikin wata biyu.
“a lokuta da dama nakan zubar da hawaye ga mutanena ganin yadda matsalar take, amma ba ni da ikon da zan ba jami’an tsaro umarni su yi maganinta.
“Akwai lokacin da ’yan ta’adda suka taba kai hari karamar hukumar Shinkafi, kuma ina zaune a nan lokacin da aka ankarar da jami’an tsaro, amma suka ki zuwa saboda wai ba a ba su umarni daga Abuja ba. Wannan ce babbar matsalar da muka fuskanta, amma mun dogara ga Allah, zai kawo mana mafita.”
Gwamna Lawal ya ce amma duk da haka, gwamnatin jihar na ba jami’an tsaro tallafin kayan aiki da kudaden gudanarwa na yau da kullum, inda ya ce bayanan hakan na nan ga duk mai bukata.
Ya kuma ce ko a wata biyu da suka gabata, gwamnatin jihar ta raba motocin sintiri guda 150 ga jami’an tsaro na sojoji, ’yan sanda da DSS da kuma sibil difens domin su inganta ayyukansu.
Gwamnan ya kuma ce ya dauko hayar mafarauta sama da 2,000 daga jihohin Borno da Yobezuwa jihar domin tallafa wa kokarin jihar na yaki da ’yan fashin dajin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Dauda Lawal Zamfara da jami an tsaro
এছাড়াও পড়ুন:
Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
A wani bidiyo daban da PUNCH Metro ta gani a Facebook, wanda Mc Pee ya wallafa, wani mutum da ake zargin dalibi ne na jami’ar ya bayyana abin da ya faru.
A cewarsa, marigayin ya roki a bar shi ya rayu kafin daga bisani wanda ake zargin ya kashe shi.
Ya ce: “Nanpon ya riga ya yanke Peter a kumatunsa yayin da yake rokon a bar shi. Lokacin da muka shiga tsakani muka ce ya daina, sai ya yi barazanar yanka duk wanda ya kusanto shi.
“Da Peter ya ga ba ya sauraron rokonsa, sai ya rungume shi yana rokonsa da kuka.
“Mun fita neman taimako amma babu wanda ya amsa mana. Da Peter ya yi kokarin tserewa sai ya fadi, Nanpon ya kamo shi ya ci gaba da saransa da adda.”
Wani kwararren masanin tsaro da yaki da ta’addanci ya wallafa a dandalin D a ranar Lahadi cewa jami’an rundunar ‘yan sandan Jihar Filato sun kama wanda ake zargin.
Ya kuma ambaci majiyoyi da suka tabbatar da faruwar lamarin ta hanyar rahoton da aka samu daga Babban Jami’in Tsaro na jami’ar.
Ya rubuta cewa, “Rundunar ‘Yansanda ta Filato ta kama wani dalibi mai shekaru 23 na Jami’ar Jos bisa zargin kashe abokinsa sannan ya binne shi a rami mara zurfi a cikin dakinsa da ke kauyen Rusau a Karamar Hukumar Jos ta Arewa.
“Majiyoyi sun tabbatar da faruwar lamarin a ranar Lahadi a Jos, inda suka danganta da rahoton da aka samu daga Babban Jami’in Tsaron jami’ar.
“A cewar majiyoyin, wanda ake zargin mai suna Dabid Nanpon Timmap, dalibi a matakin shekara ta uku a jami’ar, ya kai wa Peter Mata Mafurai, mai shekaru 22, hari da adda, ya kashe shi a gidansa.”
Zagazola ya kara da cewa, bayan samun kiran gaggawa da misalin karfe 9:30 na safiya, DPO na sashin Laranto ya jagoranci tawagar ‘yansanda zuwa wurin, inda aka kama wanda ake zargin.
“Majiyoyin sun ce bincike ya nuna cewa wanda ake zargin ya binne mamacin a cikin rami mara zurfi da ya haka a cikin dakinsa. An tono gawar kuma an kai ta dakin ajiye gawarwaki na Asibitin koyarwa na Jami’ar Bingham domin yin binciken gawar (autopsy),” in ji shi.
Ya kara da cewa, an tsare wanda ake zargin yayin da ake ci gaba da bincike domin gano hakikanin dalilin kashe abokin nasa.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA