Da ina da iko da cikin mako biyu zan magance matsalar tsaron Zamfara – Gwamna
Published: 3rd, September 2025 GMT
Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya ce da a ce yana da cikakken iko da jami’an tsaro, da zai iya magance matsalar tsaron da ta addabi jihar shi a cikin mako biyu.
Gwamnan ya kuma ce ya san dukkan inda ’yan bindigar jihar suke buya.
Da yake jawabi a cikin wani bidiyo da ya karade shafukan sada zumunta, gwamnan ya ce babban kalubalen shi a yaki da ’yan bindiga a jihar shi ne rashin cikakken iko da jami’an tsaro.
ya ce shugabannin rundunonin tsaron da ke jihar suna karbar umarni ne kawai daga hedkwatocinsu da ke Abuja, bad aga wajen shi ba.
A cewar Gwamnan, “Na rantse da Allah na san duk inda wani shugaban ’yan bindiga yake a Zamfara, kuma duk inda ya fita ya je na sani.
“Yanzu da wayata zan iya nuna muku inda wadannan ’yan ta’addan suke a yau. Amma babu abin da za mu iya yi musu.
“Wallahi a yau da ina da iko da jami’an tsaro, ina mai tabbatar maka za mu iya kawo karshen ’yan bindiga a Zamfara cikin wata biyu.
“a lokuta da dama nakan zubar da hawaye ga mutanena ganin yadda matsalar take, amma ba ni da ikon da zan ba jami’an tsaro umarni su yi maganinta.
“Akwai lokacin da ’yan ta’adda suka taba kai hari karamar hukumar Shinkafi, kuma ina zaune a nan lokacin da aka ankarar da jami’an tsaro, amma suka ki zuwa saboda wai ba a ba su umarni daga Abuja ba. Wannan ce babbar matsalar da muka fuskanta, amma mun dogara ga Allah, zai kawo mana mafita.”
Gwamna Lawal ya ce amma duk da haka, gwamnatin jihar na ba jami’an tsaro tallafin kayan aiki da kudaden gudanarwa na yau da kullum, inda ya ce bayanan hakan na nan ga duk mai bukata.
Ya kuma ce ko a wata biyu da suka gabata, gwamnatin jihar ta raba motocin sintiri guda 150 ga jami’an tsaro na sojoji, ’yan sanda da DSS da kuma sibil difens domin su inganta ayyukansu.
Gwamnan ya kuma ce ya dauko hayar mafarauta sama da 2,000 daga jihohin Borno da Yobezuwa jihar domin tallafa wa kokarin jihar na yaki da ’yan fashin dajin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Dauda Lawal Zamfara da jami an tsaro
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu Ya Janye Dokar Ta-baci A Jihar Rivers
Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da janye dokar ta-baci a Jihar Rivers daga ƙarfe 12 na daren 17 ga watan Satumban 2025.
Shugaban Ƙasar, a wata sanarwa da ya sanya wa hannu, ya ce dokar ta-bacin da ta dakatar da Gwamna, Mataimakiyarsa, da ‘yan majalisar dokokin jihar na tsawon watanni shida ta cimma manufarta na dawo da zaman lafiya a jihar.
Tinubu ya bayyana cewa ya yi amfani da Sashe na 305 na Kundin Tsarin Mulkin 1999 ne a watan Maris na 2025 sakamakon durƙushewar mulki a Jihar Rivers.
A cewarsa, rashin jituwa tsakanin Gwamna Siminalayi Fubara da Majalisar Dokokin Jihar, da kuma lalata muhimman kadarorin gwamnati sun jefa jihar cikin rikici.
“Lamarin ya kai ga Babbar Kotun Ƙoli ta bayyana a ɗaya daga cikin hukuncinta cewa babu gwamnati a Jihar Rivers.” In ji Shugaban Ƙasa.
Ya gode wa Majalisar Ƙasa bisa amincewa da wannan sanarwa, tare da yabawa Sarakuna da jama’ar jihar bisa haɗin kan da suka bayar.
Tinubu ya kuma yaba wa masu adawa da suka kalubalanci wannan mataki a kotu, yana cewa wannan shi ma wani ɓangare ne na dimokuraɗiyya.
Da yake magana kan sabuwar fahimta tsakanin manyan ‘yan siyasa a jihar, Shugaban Ƙasa ya ce babu dalilin ƙara tsawaita dokar ta-bacin.
Ya bayyana cewa Gwamna Siminalayi Fubara, da Mataimakiyarsa Ngozi Nma Odu, da Shugaban Majalisar Dokoki Martins Amaewhule da dukkan mambobin majalisar jihar za su koma bakin aiki daga 18 ga Satumban 2025.
Tinubu ya yi kira ga shugabannin siyasa a faɗin Najeriya da su ƙarfafa zaman lafiya da haɗin kai domin isar da fa’idodin dimokuraɗiyya ga al’umma.
Daga Bello Wakili