Aminiya:
2025-09-17@23:12:48 GMT

Kemi Badenoch ta shiga tsaka mai wuya kan karatun likitanci

Published: 2nd, September 2025 GMT

’Yar Najeriya kuma Shugabar Jam’iyyar Conservative a Birtaniya, Kemi Badenoch, ta shiga tsaka mai wuya kan iƙirarinta na cewa Jami’ar Stanford ta ba ta gurbin karatun horon shiga likitanci bisa rangwamen kuɗi tun tana ’yar shekara 16.

An fara sanya alamar tambaya a kan iƙirarinta ne bayan da wani tsohon jami’in kula da ɗaukar ɗalibai a jami’ar mai suna Jon Reider, ya musanta iƙirarin na Kemi Badenoch, wadda ta yi kaurin suna wajen sukar ƙasarta ta haihuwa.

Kemi Badenoch ta yi iƙirari cewa ta samu gurbin ƙaramin tallafin kuɗi daga Jami’ar Stanford, amma rashin kuɗin iyayenta ya hana ta amfani da damar.

Sai dai Jon Reider, wanda a lokacin yake kula da ɗalibai daga ƙasashen waje da tallafin karatu a Stanford, ya ƙaryata ikirarin nata.

An kai wa tsohon Ministan Shari’a Abubakar Malami hari a Kebbi NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Da Mutane Zasu Bi Wajen Neman Diyya

Ya ce: “Duk da cewa shekaru 30 sun shuɗe, amma tabbas da zan tunawa idan da mun taɓa ɗaukar wata ɗalibar Najeriya bisa wani tallafi — gaskiya ba mu yi ba,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa jami’ar ba ta ɗaukar ɗalibai bisa sakamakon SAT kaɗai, kuma ba ta bayar da tallafin ragin kuɗi ba; domin idan ɗalibi na bukatar $30,000 a shekara, ragi ba shi da amfani domin ba zai iya wucewa ba.

Haka kuma, ya ce bai taɓa samun umarnin sauke shawarar sa ba daga wani shugaba a jami’ar.

Masu suka daga cikin jam’iyyun Labour da Liberal Democrats sun buƙaci Badenoch da ta bayyana dalilin wannan iƙirarin, saboda haƙƙin jama’a ne su san gaskiya, musamman abin da ya shafi shugabar adawa.

Duk da wannan tirjiyar, Badenoch ta tsaya kan cewa ta samu tayin bisa ga sakamakon SAT ɗinta.

Ta ce: “Na tuna ranar da wasiƙun suka iso a gare ni — ba na da takardu yanzu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gurbin karatu Jami ar Stanford karatun likitanci

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

 

Wata sanarwa da Daraktan Yada Labarai da Hulda da Jama’a na Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya, Folasade Boriowo, ya fitar, ta ce a karon farko cikin shekaru da dama, daliban Nijeriya za su ci gaba da karatun tarihin Nijeriya tun daga Firamare 1 zuwa karamar Sakandare 3 yayin da daliban SSS 1 – 3 za su koyi sabon darasin da aka samar na ‘Civic and Heritage Studies’, wanda ya hada tarihin Nijeriya da Ilimin zamantakewar Jama’a.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • UNICEF Ya Ba Da Tallafin Kayayyakin Aiki Ga Cibiyoyin Lafiya A Kirikasamma
  • Kwara ETF Ya Dauki Nauyin Karatun Fitattun Dalibai A Matakin Sakandare
  • Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu
  • Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye
  • NECO ta saki sakamakon jarabawar 2025
  • NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025
  • Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • ’Yan sanda sun kama mutum 6 kan satar zinarin N109m a Kebbi
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • Ɗangote zai gina ɗakunan kwanan ɗalibai 250  a Jami’ar Ilorin