Aminiya:
2025-11-02@21:10:42 GMT

Girgizar ƙasa ta kashe mutum 610 a Afghanistan

Published: 1st, September 2025 GMT

Aƙalla mutum 610 ne suka rasa rayukansu yayin da wasu sama da 1,300 suka jikkata sakamakon girgizar ƙasa mai ƙarfi da ta afku a ƙasar Afghanistan.

Rahotanni daga hukumomi da kafafen watsa labarai na duniya sun ce ibtila’in ya auku ne a yankin gabashin ƙasar Afghanistan, kusa da iyakarta da Pakistan.

Rahoton Hukumar Binciken Ƙasa ta Amurka (USGS) ya bayyana cewa ƙarfin girgizar ƙasar ta kai matakin 6.

0, kuma cibiyar ta kasance a wani yanki mai tazarar kilomita 27 daga birnin Jalalabad, inda ake da yawan jama’a kimanin 300,000.

An gano cewa girgizar ta afku a zurfin kilomita takwas kacal daga saman ƙasa, wanda hakan kan ƙara tsananta illarta.

Rushe Kasuwar Alaba Rago: Ya kamata shugabannin Arewa su sa baki An ƙone wata mata ƙurmus kan yi wa Annabi ɓatanci a Neja

Kamfanin Dillancin Labarai na AP ya rawaito cewa akwai yiwuwar adadin mutanen da suka mutu zai ƙaru yayin da ake ci gaba da binciko gawarwaki da kuma ceton waɗanda ke cikin ɓaraguzan gine-gine.

Haka zalika, New York Times ta ce an ji girgizar a Kabul — babban birnin Afghanistan — da ke tazarar kilomita 160 daga Jalalabad, duk da cewa ba a tabbatar da samun mace-mace a can ba.

Mai magana da yawun gwamnatin Taliban, Zabihullah Mujahid, ya wallafa a shafinsa na X cewa, “Muna cikin alhini kan asarar rayuka da asarar dukiya da wannan girgizar ƙasa ta haddasa a wasu yankunan gabashin ƙasarmu. Jami’ai da mazauna yankin suna ci gaba da aikin ceto.”

Me ke kawo yawon girgizar ƙasa a Afghanistan?

Afghanistan na fuskantar yawan girgizar ƙasa saboda matsayinta na tectonic.

Wannan yanayi ne da ke haifar da fashewar ƙasa akai-akai, musamman a yankunan tsaunuka da ke gabashin ƙasar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Girgizar ƙasa girgizar ƙasa

এছাড়াও পড়ুন:

Kasashen Pakistan Da Afghanistan Sun Tsawaita Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta

Bayan duguwar tattaunawa a birnin Istanbul na kasar turkiya kasashen pakisatan da Afghanistan sun amince da batun tsawaita dakatar da bude wuta a tsakanin iyakokin kasashen,  bayan da kasashen turkiya da Qatar suka shiga tsakanin domin samun daidaito.

Gwabzawa a iyakokin kasashen biyu dake mukwabtaka a yan makwannin nan yana barazana sosai ga zaman lafiyar yankin, sai dai wannan yarjejeniyar za ta hana yaduwar fadan da kuma kara samun hadin guiwa kan tsaron iyakokin.

Zabiullah mujahid kakakin kungiyar Taliban ya tabbatar da kulla yarjejeniyar, kuma yace Kabul tana son samun kyakkyawar dangantaa da dukkan kasashen dake makwabtaka da ita, musamman kasar Pakistan bisa mutunta juna da kuma rashin tsoma baki a harkokin cikin gidan kasashen.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka M D Duniya Tayi Gargadi Game Da Gwajin Nukiliya Da Amurka Ta Sanar Za ta yi October 31, 2025 Sudan Ta Yi Kira Ga Kwamitin Tsaro Da Ya Ayyana RSF A Matsayin Kungiyar ‘Yan Ta’adda October 31, 2025 Araqchi: Gwajin Makaman Nukiliya Na Amurka Babbar Barazana Ce Ga Duniya October 31, 2025 Masar da Eritrea Sun Tattauna Bukatar Tallafawa Kasar Sudan October 31, 2025 Shugaban Lebanon Ya Umarci Sojoji Da Su Fuskanci Kutsen Na Isra’ila A Kudancin Kasar October 31, 2025 Madagascar Ta Sanar da Kafa Sabuwar Gwamnati Tare da Manyan ‘Yan Adawa October 31, 2025 Iran ta yi fatali da kalamman IAEA Kan Shirin Nukiliyarta October 30, 2025 Trump Ya Umarci Ma’aikatar Yakin Amurka Ta koma gwajin makaman nukiliya October 30, 2025 Isra’ila ta amince da fadada matsugunai a Yammacin Kogin Jordan October 30, 2025 Gaza: hare-haren Isra’ila sun kashe mutane 100 Cikin Kwanaki Biyu October 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba
  • Tsaro: Taimakonmu Amurka ya kamata ta yi maimakon barazana — Kwankwaso
  • Tsaro: Taimakonmu Amurka ya kamata ta yi maimakon ba barazana ba — Kwankwaso
  • Kisan Kiristoci: Ba zan yaƙi ƙasar iyayena kan labaran ƙarya ba — Sojan Amurka
  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • Kisan Kiristoci: Za mu kai hari Najeriya — Trump
  • Wasu Yan Ta’adda Sun Kashe Dakarun Sa Kai 2 A Kudu Maso Gabashin Iran
  • Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
  • An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano
  • Kasashen Pakistan Da Afghanistan Sun Tsawaita Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta