Rushe Kasuwar Alaba Rago: Ya kamata shugabannin Arewa su sa baki
Published: 1st, September 2025 GMT
Ƙungiyar Arewa ta ’Yan Jarida (ABMPF) ta roƙi Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya dakatar da rushe Kasuwar Alaba Rago da Gwamnatin Jihar Legas ta fara, tana mai cewa matakin ya jawo asarar biliyoyin naira tare da barin dubban ’yan kasuwa cikin halin ƙaƙa-ni-ka-yi.
Shugaban Ƙungiyar, Alhaji Abdullahi Yelwa, ya ce rusau ɗin ya haddasa wa ’yan kasuwar asarar kimanin Naira biliyan 20, tare da ruguza shaguna da wuraren ibada fiye da 40, abin da ya ce “bai dace ba kuma yana iya jawo rikicin ƙabilanci.
Kungiyar ta roƙi gwamnonin Arewa, ’yan majalisa da sarakuna na gargajiya su shiga wajen tabbatar da kare haƙƙin ’yan Arewa da suke zaune a Legas.
Haka kuma ta yi kira ga Gwamna Babajide Sanwo-Olu ya sake duba matakin, ya samar da diyya da shirin sake mazauna kasuwar.
Gargaɗi kan zagin Sahabban Annabi Muhammad (SAW) An ƙone wata mata ƙurmus kan yi wa Annabi ɓatanci a NejaSai dai Gwamnatin Jihar Legas ta kare kanta, tana mai cewa aikin na daga cikin shirin gyaran birni da ake aiwatarwa domin ƙara inganta tsaro da tsarin kasuwanni.
“Ba a yi wannan rushewar saboda ƙabila ko addini ba,” in ji mai magana da yawun Ma’aikatar Tsara Birane ta jihar.
“Mun fara gyara wuraren da ba su dace ba don samar da sabuwar kasuwa mai tsari da aminci ga kowa.”
Gwamnatin ta ce tana nazarin matakan diyya da wurin da za a koma ga ’yan kasuwar da abin ya shafa, kodayake ba ta fitar da cikakken shiri ba tukuna.
Amma ABMPF ta yi watsi da bayanin gwamnatin, tana mai cewa ba a bi ƙa’ida wajen aiwatar da rusau ɗin ba, sannan ba a bai wa ’yan kasuwa isasshen lokaci ko inda za su koma ba.
“Abin takaici ne a kira al’ummar Arewa mazauna Alaba na tsawon shekara 80 da ’yan fiye da haka ’yan haya ko masu zama na wucin gadi da za a iya koran su duk lokacin da aka so,” in ji ƙungiyar.
Ta ƙara da cewa matakin yana nuna yunƙurin kawar da ’yan Arewa da ’yan yankin Gabas daga Legas, abin da zai iya haifar da rikice-rikice a wasu jihohin Arewa inda Yarbawa ke zaune cikin lumana.
Tasirin tattalin arzikiKasuwar Alaba Rago, wadda ta mamaye sama da hekta 10, wadda ta kasance cibiyar kasuwanci ga ’yan Arewa tun kafin samun ’yancin kai, ta tara dillalan dabbobi, hatsi da kayan gona da ake kawo su daga sassa daban-daban na ƙasar nan.
Masana tattalin arziki na gargaɗin cewa ruguza kasuwar zai iya shafar harkokin kasuwanci, kawo hauhawar farashi da rage harajin da jihar take samu daga irin waɗannan kasuwanni.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: diyya kasuwa Kasuwar Alaba Rago Yan Arewa
এছাড়াও পড়ুন:
MDD Tana Sa Ido Akan Kashe-kashen Da Ake Yi A Zaben Kasar Tanzania
Hukumar kare hakkin bil’adam dake karkashin MDD ya sanar da cewa tana sa ido akan kashe-kashe da rashin adalcin da ake yi a karkashin zaben shugaban kas ana kasar Tanzania. Tun a ranar Larabar da ta gabata ne dai da ake zaben rikici ya barke a kasar sabod kin amincewar ‘yan hamayya akan yadda zaben zai gudana ba tare da manyan ‘yan takara ba. Shugabar kasar Samia Suluhu Hassan ce dai babbar ‘yar takara. Babbar jam’iyyar adawa ta sanar da cewa fiye da mutane 700 ne aka kashe a fadin kasar da ake Zanga-zanga. Shugaban ofishin hukumar kare hakkin bil’adama na MDD Seif Magango ya sanar da cewa; Sun karbi rahoranni daga majiya mai tush akan cewa a kalla an kashe mutane 10. Hukumar ta yi kira ga jami’an tsaron kasar ta Tanzania da su daina amfani da karfi a inda bai dace ba, daga cikin har da amfani da makamai akan masu Zanga-zanga. Haka nan kuma sun yi kira ga masu Zanga-zanga da su yi a cikin ruwan sanyi. Ita kuwa kungiyar kare hakkin bil’adama ta “Amnesty International” ta ce nata rahoton ya tabbatar mata da cewa an kashe abinda bai kasa mutane 100 ba. Tuni dai aka kafa dokar ta baci da hana zirga-zarga a babban birnin ksar Darus-salam, ana kuma rufe hanyoyin sadarwa na interten daga lokaci zuwa lokaci. Har ila yau MDD tana yin kira da a saki dukkanin wadanda ake tsare da su.Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Gaza: Daga Tsagaita Wuta Zuwa Yanzu Fiye Da Mutane 200 Ne Su Ka Yi Shahada November 1, 2025 Shugaban Kasar Najeriya Ya Mayar Da Martani Ga Takwaransa Na Amurka Akan Rikicin Addini November 1, 2025 Iran ta damu da halin da ake ciki a yankin El Fasher na Sudan November 1, 2025 Kwamitin Tsaron MDD ya goyi bayan shirin Morocco game da yankin Yammacin Sahara November 1, 2025 Samia Suluhu Hassan ta lashe zaben shugaban kasa a Tanzaniya November 1, 2025 Najeriya ta musanta ikirarin Trump, na cewa Kristoci na fuskantar babbar barazana a kasar November 1, 2025 Majalisar Dinkin Duniya ta damu da hare-haren Amurka a Caribbean da Pacific November 1, 2025 Israila Ta Kai Hari Kan Ofishin kungiyar UNICEF Dake Gaza A November 1, 2025 Amurka Na Shirin Kai Hari Kan Kasar Venzuwela A Kowanne Lokaci November 1, 2025 Iran Ta Sanya Da Ranar 30 Ga Watan Nuwamba A Matsayin Ranar Kasa Ta Tsibirai 3 October 31, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci