Gwamnatin Sakkwato za ta fara biyan masallatan Juma’a kuɗi duk wata
Published: 31st, August 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Sakkwato ta bayyana cewa za ta riƙa bai wa kowane masallacin Juma’a a jihar kuɗi daga Naira 300,000 zuwa 500,000 duk wata domin tallafa musu.
Haka kuma gwamnatin za ta riƙa biyan limaman masallatan, na’ibansu da ladanai alawus na kowane wata domin sauƙaƙa wa hidimominsu.
Zaɓen Ribas: APC ta yi nasara a ƙananan hukumomi 20, PDP ta samu 3 Sojoji sun kashe mayaƙan Boko Haram 12, sun ƙwato makamai a BornoMai magana da yawun gwamnatin, Abubakar Bawa ne, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa.
Ya ce manufar shirin shi ne ƙarfafa karatun Alƙur’ani da koyar da ilimin addini ga yara da matasa a jihar.
Gwamna Ahmed Aliyu, ya sanar da wannan mataki ne a ranar Asabar yayin yaye ɗalibai 111 da suka kammala haddar Alƙur’ani a makarantar gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi da ke Sakkwato.
Ya ce alawus ɗin zai taimaka wajen ba malamai damar yin nazari da ci gaba da koyar da darusan addini.
Gwamnan ya ƙara da cewa gwamnatinsa ta bayar da kwangilar gyara masallatai 65 na Juma’a, inda aka kammala 25, kuma aka riga aka buɗe 15 daga cikinsu.
Ya ce kula da harkokin addinin Musulunci na daga cikin manufofin gwamnatin sa, kuma ya ce yana da muhimmanci bayan batun tsaro.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Alawus gwamnati Sakkwato
এছাড়াও পড়ুন:
Najeriya Na Asarar Dala Biliyan 10 Bayan Girbi Duk Shekara- Gwamnatin Tarayya
Gwamnatin Tarayya ta ce Najeriya na rasa sama da Dala Biliyan 10 duk shekara sakamakon asarar amfanin gona bayan girbi.
Ministan Noma Sanata Abubakar Kyari ne ya bayyana haka a wajen kaddamar da shirin Hanyar Inganta Noma da Kayayyakin Mire Rayuwa a Yankunan Karkara G.R.A.I.N a ƙaramar hukumar Birnin Kudu ta Jihar Jigawa.
Ya ce asarar na faruwa ne saboda rashin ingantattun wuraren ajiya, karancin ababen more rayuwa, sauyin yanayi da kuma ambaliya.
Kyari ya bayyana cewa noma na bada gudunmawar kashi 24 bisa 100 na Jimillar Darajar Kayayyaki da Ayyuka da Kasa ta Samar a Cikin Shekara GDP, inda ƙananan manoma ke samar da sama da kashi 70 bisa 100 na abincin da ake ci a ƙasa.
Ya jaddada cewa gwamnati za ta tallafa musu da kayan noma na zamani da wuraran kasuwanci domin inganta tattalin arziki.
A nasa jawabin, Gwamna Umar Namadi na Jigawa ya yaba da samun Cibiyar Cigaban Karakara ta Pulse ta farko a Jigawa, yana mai cewa za ta kawo sauyi a harkar noma da rayuwar jama’ar karkara.
Haka zalika, shi ma Ministan Harkokin Waje, Yusuf Tuggar, ya ce haɗin gwiwar gwamnati da masu zaman kansu zai taimaka wajen ci gaban tattalin arziki.
Shugaban ƙaramar hukumar Birnin Kudu, Alhaji Builder Muhammad Uba, ya jaddada goyon bayansa ga shirin Renewed Hope Agenda na Shugaba Tinubu tare da yabawa gwamnatin Namadi kan sauya fasalin noma a jihar.
Usman Muhammad Zaria