Gwamnatin Sakkwato za ta fara biyan masallatan Juma’a kuɗi duk wata
Published: 31st, August 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Sakkwato ta bayyana cewa za ta riƙa bai wa kowane masallacin Juma’a a jihar kuɗi daga Naira 300,000 zuwa 500,000 duk wata domin tallafa musu.
Haka kuma gwamnatin za ta riƙa biyan limaman masallatan, na’ibansu da ladanai alawus na kowane wata domin sauƙaƙa wa hidimominsu.
Zaɓen Ribas: APC ta yi nasara a ƙananan hukumomi 20, PDP ta samu 3 Sojoji sun kashe mayaƙan Boko Haram 12, sun ƙwato makamai a BornoMai magana da yawun gwamnatin, Abubakar Bawa ne, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa.
Ya ce manufar shirin shi ne ƙarfafa karatun Alƙur’ani da koyar da ilimin addini ga yara da matasa a jihar.
Gwamna Ahmed Aliyu, ya sanar da wannan mataki ne a ranar Asabar yayin yaye ɗalibai 111 da suka kammala haddar Alƙur’ani a makarantar gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi da ke Sakkwato.
Ya ce alawus ɗin zai taimaka wajen ba malamai damar yin nazari da ci gaba da koyar da darusan addini.
Gwamnan ya ƙara da cewa gwamnatinsa ta bayar da kwangilar gyara masallatai 65 na Juma’a, inda aka kammala 25, kuma aka riga aka buɗe 15 daga cikinsu.
Ya ce kula da harkokin addinin Musulunci na daga cikin manufofin gwamnatin sa, kuma ya ce yana da muhimmanci bayan batun tsaro.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Alawus gwamnati Sakkwato
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Jihar Kwara Ta Kafa Kwamitoci 2 Don Tantance Wadanda Suka Yi Ritaya
Daga Ali Muhammad Rabi’u
Gwamnatin Jihar Kwara ta kafa kwamitoci biyu domin tantance bayanan wadanda suka yi ritaya a matakin jiha da kananan hukumomi.
A cikin wata sanarwa da Kwamishinar Kudi ta jihar, Dakta Hauwa Nuru ta fitar, ta bayyana cewa kwamitocin za su tantance tare da tabbatar da sahihancin bayanan wadanda suka yi ritaya, domin a biya su bisa lokacin da suka bar aikin gwamnati.
A cewarta, kwamitin mutum takwas da aka kafa don kula da kudaden ritaya na matakin jiha zai kasance karkashin jagorancin Mai Duba Asusun Jiha, wato (Auditor General), yayin da wanda ke kula da matakin kananan hukumomi zai kasance karkashin Mai Duba Asusun Kananan Hukumomi.
Sanarwar ta bayyana cewa babban burin kwamitocin shi ne tabbatar da cewa an tattara bayanan masu ritaya bisa gaskiya da adalci, tare da biyan su kai tsaye ta asusun ajiyar banki.
Ta kara da cewa, mambobin kwamitocin sun hada da wakilan tsofaffin manyan sakatarorin, kungiyar tsofaffin ma’aikata, Kungiyar Kwadago ta Najeriya (NLC), da kungiyar kwadago ta TUC, da sauransu.