Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 136
Published: 31st, August 2025 GMT
136- Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka barkammu da sake saduwa a cikin shirimmu na kissoshin rayuwa shiri wanda yake kawo maku kissoshi wadanda suka zo cikin alkur’ani mai girma, ko kuma cikin wasu littafan wadanda suka hada da littafin Dastane, Rastan na Aya. Shahid Murtada Muttahari, ko kuma cikin littafin Mathnawa na maulana jalaluddin Rumi.
////…Madallah, masu sauraro idan kuna tare da mu a cikin shirimmu da ya gabata, a kuma cikin sirar Imam Hassan Al-mujtapa (a) jikan manzon All..(s) da muke kawo maku, a cikin shirimmu da ya gabata, mun bayyana yadda aka fara yakin Siffin yakin da ya sauya tarihin musulunci, yakin da, da ba’a ya shi ba da duniyar musulmi da kuma sauran mutane ba haka zai kasance ba. Sabu a siffin ne aka kulla makirce-makirce wadanda suka sauya fuskan addinin All..zuwa addinin sarakunan banu umayya da Abba siyawa daga bayan.
Bayan da Imam Ali (a) ya debe kauna dawowan Mu’awiya, sai ya kulla tutoci, ya bawa kwamandojin sojijinsa wadanda suka hada da Malikul Ashtar, Ammar dan yasir, Ash’ash dan kais alkindi Abdullahi dan Abbas da sauransu, haka ma mu;wiya ya rarraba tutocinsa ga kwamandujikinsa, Ubaidullahi dan Umar Abdullahi dan Amru dan Ashi, da Dhahaak da sauransu.
Imam (a) yayi masu khuduba wanda ya saba yi kafin yaki, kamar yadda yayi A jamal musamman sanin wannan yaki tsakanin musulmine, don haka ya bayyana musu, sabbin dokokin yaki wadanda basu taba saninsu, wadanda suka hada da, cewa kada su bi wanda ya juya baya daga yakin, kada su karasa wanda yi rauni, kada su shiga tentunansu na tafiya, kada su daga labule kada su shiga wani gida ba tare da sallama ba, kada su dauki wani abu daga wajensu sai abinda ya shafi yaki wato kamar takobi ko dawakansu na yaki, amma duk sauran gado ne ga magadansu.
Sannan aka fara yaki jefi jefi saboda Imam (a) yana fatan mu’awiya ya dawo daga dagawarsa ya tuba. Suna cikin wannan halin har watan muharram ya shigo, suna daina yaki. Na wata guda, sannan a cikin wannan lokacin sukan shudanya da juna babu fada a lokacinda Safar ya shigo sai suka koma yaki. Ana cikin wannan halin ne, Mu’awiya ya aiki Ubaidullahi dan Umar ya je ya kodaitar da Imam Hassan (a) ko muce ya yaudare shi, kan ya dawo bangaren su ya bar babansa Immam Ali (a), saboda ya kashewa kuraishawa iyayensu a yake-yaken da yayi tare da manzon All..(s), sai Imam hassan ya ce babansa yayi dai dai tunda a kan tafarkin All..ya kashe su. A nan ne sai yace masa mu’awiya ya yi alkawalin zai bashi khalifanci idan ya koma bangarensa. A lokacin Imam Hassan (a) ya ji wadannan kalaman, sai ya daka masa tsawa, ya kuma bayyana masa cewa hakan ba zai taba yi yu wa ba.
Sai Imam yayi masa wani kallo, na fushi a fuskansa, sai yace masa nan gaba kadan za’a kashe ka wannan yakin. Ya kara da cewa:
{Sai dai ina son sanar da kai, za’a kashe ka yau ko gobe. Imma shaitan ya kawata maka, ya yaudareka, sai da ya fito da kai, kana dauke da wannan halin, matan sham zasu ga matsayinka da , kuma All..zai turbude fuskanka matacce.)
Sai Ubaidullah ya koma wajen Mu’awiya ya kuma fada masa abinda ya fada da martanin da ya mayar masa. Sai Mu’awiya ya ce: Lallai shi dan babansa ne.
Daga nan sai Ubaidullah ya fita yaki tare da makiya, sai ya gamu da wani mutum wanda ake kira Fazza Nabil daga Hamdan, sai ya kashe shi, sannan ya zauna a wurin, ya jingina da gawar Ubaidullahi dan Umar, sannan ya daura dokinsa a kafar gawar.
Sai Imam Hassan (a) ya zo wurin tare da wasu daga cikin magoya bayansa. Sai ya masu ku duba waye yake jingine da gawannan ? sai suka je suka gani suka dawo suka fada masa, wani mutumin Hamadan ne kuma gawar ta Ubaidullahi dan Umar ne, sai Imam ya yi farinciki da hakan. Ya fadi hakan yana mai murmuci: {Godiya ta tabbata kan Hakan.}
Don haka daga karshe dai Ubaidullahi dan Umar ya hadu da ajalinsa yana mai yakar All..da manzonsa (s). kuma mai zaluntar musulmi, kuma a matsayin dan tawaye ga shugaban musulmi Aliyu dan Abitalib(a).
Daga nan sai yaki na gama gari, ko gaba daya. A lokacin da Imam (a) ya ga cewa babu alamun mu’awiya zai dawo sai ya sake tsara sojojinsa ta yadda za’a shiga yakin yaki n agama gari. Bayan da Mu’awi ya ga haka shi sai ya sake tsara sojojinsa.
Ana cikin wannan halin sai Imam al-Hassan (a), ya fara kaiwa sojojin Mu’awiya hare-hare, a lokacinda Imam ya ga haka sai ya damu sannan ya fadawa wadanda suke kusa da shi,
{Ku kama mani wannan yaron, kada ya halakani, don ni ina matukan kare wadan nan –Al-hassan da al-Al-hussain (a) daga mutuwa, don kada zuriyyar manzon All..(s) ya yanke a kansu}.
Don haka yaki ya barke tsakanin rundunonin biyu, har saida mutane kowa ya ji tsoron mutuwa, kowa yana iya mutuwa a ko yaushe, sai an kutsa cikin bangaren damar sojojin Imam (a). tsakiyar rundunarsa ta yi rauni. Kuma faduwa ta bayyana a wajenta.
Sai ya kira Sahal dan Hunaif, a lokacinda ya zo, sai yace masa ya koma ta dama tareda wadanda suke tare da shi. Da suka isa, sai sojojin sham suka far ma su, sai suka tare su suka kuma tarwatsu. Sai suka koma ta hagu.
Imam (s) da kansa yana shiga yakin , sannan yayansa suna tare da shi suna tare masa duk wasu makaman da suke zuwa kansa. Sai wani mai suna Ahmar Kisan daga cikin bayin Banu Umayya, ya nufi Imam (a), yana cewa sai ya kasashe, ya yi ta kutsawa har ya zo kusa da Imam (a) sai ya kamashi ya daga sama ya jefa shi a kansa yakarya masa ya karya kafadu da hannayensa, Imam Hussain (a) da Muhamm dan Hanafiyya suka karasa shi.
Sai wasu Jama’a daga sojojin sham sun zo kusa da Imam (a) Sai Imam Hassan (a) Yace masa: Da ka dan gushe zuwa kusa da sojojimmu (wato Bani Rabee,) daga cikin mutanemmu. Sai Imam Ali (a) ya fahinci abinda yake nufi: Sai ya fadawa Imam Hassan a hankali yana cewa
{Ya da na, babanka yana da wata rana, wanda ba zai ketareta ba, kuma kokari ba zai nesantata daga gareta ba, kuma takwa ba zai jinkirta zuwanta gareshi ba, Lalle wallahi Babanka bai damu da fadawa mutuwa ba ko mutuwa ta fada masa ba}
Don haka bayan da sojojin Imam suka tarwatse suka bar Imam (a) tare da yayansa, sai Malik dan Ashtar, yayi sauri ya zo wajensa don kada makiya su kashe shi, a lokacinda ya iso sai Imam (a) ya ca masa
{Ya Maliku, sai ya masa –labbai-Ka je wajen wadan nan mutane, ka fada masu cewa: Ina ne gudunku daga mutuwa, Wanda rayuwa bazaku taba gagareta zuwa rayuwa ba, , wacce itama ba zata rege kowa daga cikinku ba.?}.
Sai Malik ya je wajen wadanda suka tarwatse a gaban Imam suka barshi a cikin makiyansa, ya kirasa ya fada masu sakon Imam, sannan yayi ta masu jawabi, masu nishadantarwa, wanda kuma ya sake basu karfin giwa, sai kuma suka dawo wajensa, ya sake nanata masu kan cewa shi ne Malik dan Ashtar, wansa suka sani da jarunta da kuma iya yaki.
Sannan da ya samu ya sake tarasu, suka tunkari sojojin Mu’awiya saida suka dangana da haimarsa, mu’awiya ya fara shirin gudu. Don kada Malik ya riske shi.
A lokacinda Mu’awiya ya ga raunin da ya bayyana a sojojinsa, ya kira masu shawara da shi wato Amru dan Asee, don sanin abinda zasu yi.
A dayan bangaren kuma Ammar dan yasir ya ga yadda kawukan mutane suke fadawa a cikin yakin, kasar Siffin gaba daya y ajika da jinin mutane, daga cikin muminai da Fasikai. Ko azzalumai. da kuma tsananin da ake ciki sai ya fada cikin tunani yana cewa:
Manzon All..(s) yayi gaskiya…wannan itace ranar da manzon All..(s) ya yi masa bushara da shahada,. Yana cewa tabbas wadannan suke azzalumai (kamar yadda manzon All..) ya kirasu. Wannan it ace ranar da manzon All..(a) yayi mani alkawali, gas hi na kusan shekara 90 a duniya me neke jira. ? Rahamarka ya Ubangiji! Hakika ni ina shaukin haduwa da yan’uwana wadanda suka rikani a Imani, ..da sannu zan hadu da Ubangijina, ina mai jihadi da makiyansa, a gaban waliyyinsa kuma wasiyin manzonsa, (s),kuma khalifansa a bayansa.To lalle ina ganin yau ce ranar da manzon All..(s) yayi mani alkawali.
Daga nan yayi ta kallon tutocin a yakin sai ya ga cewa, tutocinsu sun yi kama da tutocin manzon All…(s) a badar da uhudu da kuma Hunain, a yayinda dayan bangaren kuma ya yi kama da tutocin mushrikai da rundunoni.
Masu sauraro a nan zamu dasa aya sai kuma wata fitowa idan All..ya kaimu wassalamu Alaikum wa vrahamatullahi wa barakatuhu.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran Ta Sami Nasarar A Kan Amurka A Gasar Volleyball Na Kasa Da Kasa August 31, 2025 Rasha Tace: Masu Son Yaki A Turai Suna Zangon Kasa Ga Kokarin Trump Na Kawo Karshen Yaki A Ukraine August 31, 2025 AU Da WHO Zasu Hada Kai Don Yakar Cutar Kolera A Nahiyar Afirka August 31, 2025 Almashat: Yemen Za Ta Dauki Fansar Jinin Shahidanta A Kan Sahyuniyawa August 31, 2025 Iran ta yi Allawadai da kisan jami’an gwamnatin Yemen da Isra’ila ta yi August 31, 2025 Yemen: Firayi Ministan da wasu ministoci sun yi shahada a wani harin Isra’ila August 31, 2025 Argentina: Lauyoyi sun bukaci a cafke Netanyahu a kan laifukan yaki August 31, 2025 Sudan: Hamedti ya yi rantsuwar shugabantar gwamnati mai kishiyantar gwamnatin kasar August 31, 2025 Shugaban Kasar Iran Ya Ce: Ba Za Su Kyale A Lalata Alakar Iran Da Armeniya Ba August 30, 2025 Larijani: Iran Tana Adawa Da Juya Akalar Siyasar Yankin Daga Wasu Masu Son Baba-Kere August 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunciউৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Ubaidullahi dan Umar a cikin wannan Masu sauraro wadanda suka wannan halin masu sauraro mu awiya ya Mu awiya ya
এছাড়াও পড়ুন:
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP
A zantawar Sule Lamido da BBC, ya bayyana cewa; an yi masa kora da hali a hedikwatar jam’iyyar ta PDP.
Ya kara da cewa, ya je hedikwatar jam’iyyar PDP ne; domin karbar fom na takarar shugabancin PDP, sai ya samu ofishin da ya kamata ya karba a kulle, da ya tambaya sai aka ce da shi, a hannun gwamnan Adamawa kadai zai samu fom din.
Lamido ya ci gaba da cewa, ba ya fata a kai ga matakin da za a hana shi shiga takarar, “domin ina tunanin rigimar cikin gida ce, sannan kuma za mu iya samun maslaha a cikin gidan. Amma idan hakan bai yiwu ba, daga nan kuma na san me zan yi,” in ji shi.
Haka zalika, Sule Lamido ya ce; a shirye yake ya tsaya takarar shugabancin jam’iyyar a zaben da za a yi lokacin babban taron jam’iyyar a watan Nuwamban wannan shekara a birnin Ibadan na Jihar Oyo.
Bugu da kari, Lamidon ya sha alwashin tafiya kotu idan har aka ki sayar masa da fom din tsayawa takarar.
Kazalika, rahotanni sun tabbatar da cewa; tuni tsohon ministan ayyuka na musamman, Kabiru Tanimu Turaki ya yanki nasa fom din, a daidai lokacin da aka ki sayar wa da tsohon gwamnan na Jigawa fom din takarar shugabancin jam’iyyar ta hamayya, wato PDP.
Har wa yau, Jam’iyyar PDP ta sanar da dage tantance dan takara daga ranar Talata zuwa wani lokaci nan gaba, duk da cewa; jam’iyyar ba ta fadi dalilin yin hakan ba.
Haka nan, sanar da Kabiru Tanimu Turaki a matsayin dantakarar maslaha daga Arewacin Nijeriya ya bar baya da kura, inda wasu daga cikin shugabannin jam’iyyar PDP na shiyyar Arewa maso yammacin kasar, shiyyar da Turaki ya fito suka yi watsi da matakin da gwamnoni suka dauka.
Kazalika, shugaban jam’iyyar PDP na Jihar Sakkwato, Muhammad Bello Aliyu na cikin shugabannin da suka yi fatali da matakin da gwamnonin suka dauka, saboda a cewarsa, ba a ba su damar zama su tattauna ba, gabannin tsayar da Turakin. Kana kuma, an sake samun wasu jiga-jigan jam’iyyar daga Jihar Kebbi da suka yi fatali da wannan maslahar.
Dangane da wanan sabuwar rigima ko rikici, malami a kwalejin ilimi ta share fagen shiga jami’a da ke Kano kuma mai sharhi kan al’amuran yau da kullum, Dakta Kabiru Sa’id Sufi ya ce; ana neman fama karaya ne a yunkurin gyara targade.
“Mun dauka cewa, tunda aka zo batun zaben shugabanci, matsalolin da jam’iyyar ke ciki sun kusa zuwa karse, musammman ganin har an yi kokarin rarraba mukamai zuwa shiyya-shiyya, amma kuma sai hakan ya bar baya da kura.
“Yanzu haka, an fara samun korafi daga bangarori da dama, ciki har da daga wadanda ake ganin ba su da wata matsala.”
Haka nan, ya kara da ce; hana Sule Lamido sayen fom din takarar shugabancin jam’iyyar, wani babban al’amari ne, domin kuwa a cewar tasa; hakan ya kara haifar da rashin gamsuwa a tsakanin ‘ya’yan jam’iyyar.
Ya ce, “Akwai da ma wasu da suke ganin an lasa musu zuma a baki a Arewacin kasar na tsayawa takara, sai daga baya suka gane cewa, ba da gaske ake ba. Idan aka duba, za a ga akwai rashin gamsuwa daga bangarori da yawa. Ko bangaren Shekarau ma, sun nuna rashin gamsuwa da yadda ake tafiyar da al’amuran.”
ShareTweetSendShare MASU ALAKA