Chelsea ta kammala ɗaukar Garnacho daga Manchester United
Published: 31st, August 2025 GMT
Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Chelsea ta tabbatar da ɗaukar ɗan wasan gaban Manchester United, Alejandro Garnacho, kan kuɗin da ya kai kusan fam miliyan 85 (£85m).
Rahotanni sun bayyana cewa ɗan wasan na ƙasar Argentina ya rattaba hannu kan kwantiragin zama a Stamford Bridge har zuwa shekarar 2032.
Hamas ta tabbatar da mutuwar jagoranta a Gaza, Mohammed Sinwar Xi na karɓar baƙuncin taron SCO a ChinaGarnacho, mai shekara 21, zai riƙa ɗaukar albashin fam 250,000 duk mako, kwatankwacin Naira miliyan 500 a kuɗin Nijeriya, lamarin ya sanya shi a sahun manyan ’yan wasa mafiya albashi a Stamford Bridge.
A bara ne tauraruwarsa ta haska a Manchester United, bayan ya ci ƙwallo 11 ya kuma ba da gudunmawar zura wasu 10 a raga.
A jimilla, ya buga wasanni 144 tun daga lokacin da aka ɗaukoshi daga Atlético Madrid a 2020, inda ya ci ƙwallo 26.
Ana iya tuna cewa Garnacho yana cikin ’yan wasa biyar da suka nemi barin United, ciki har da Marcus Rashford, Antony, Tyrell Malacia da Jadon Sancho, bayan wata matsala da ta shafi sabon tsarin koci a Old Trafford.
Kociyan Chelsea, Enzo Maresca, ya bayyana farin ciki da wannan cafane da aka yi, inda ya ce Garnacho zai ƙara wa ƙungiyar kuzari da saurin kai hare-haren a wasanninta.
“Ɗan wasa ne da yake iya sauya salon wasanni da kansa, kuma hakan zai taimaka wajen dawo da Chelsea cikin sahun manyan ƙungiyoyin masu neman kofuna,” in ji shi.
Masu sharhi sun ce wannan matakin zai ƙara armashi da zafi a gasar Premier League, musamman ganin yadda Garnacho ya saba taka rawar nuna kansa a manyan wasanni.
Sai dai da dama daga cikin magoya bayan Manchester United sun nuna takaicinsu kan cefanar da ɗan wasan da aka yi, inda suke ganin bai kamata a sayar da shi ba saboda a gina ƙungiyar da shi tare da sauran matasan ’yan wasan da ke nuna hazaƙa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Alejandro Garnacho Enzo Maresca
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai
A jawabinsa yayin taron, Gwamna Sani ya gabatar da kasida mai taken: “Gina Haɗin Gwiwa Domin Ci Gaban Kowa”, inda ya bayyana yadda Jihar Kaduna ke ci gaba da samun nasara a fannoni da dama kamar gyaran birane, bunƙasa noma, da tsarin tallafiwa jama’a.
Gwamnan Ya ce tsarin ci gaban jihar yana dogara ne kan faɗaɗa damar tattalin arziki da kare marasa ƙarfi, da ƙarfafa jama’a su samu nasara a rayuwarsu.
Gwamna Uba Sani, ya kuma halarci shirin baje koli na birnin Dubai mai taken : “Sauya Arewa a Nijeriya: Jagoranci, Ƙirƙira, da Tasirin Zamantakewa”, inda nan ma ya jaddada cewa jagoranci mai nagarta da amfani da fasaha a mulki suna da matuƙar muhimmanci wajen buɗe damarmaki ga mutane da birane.
A yayin taron, Gwamnan ya gudanar da wata ganawa ta musamman da Marwan Bin Galita, Darakta Janar na birnin Dubai inda suka tattauna batutuwan haɗin gwiwa a fannin kirkirar makamashin sharar gida da kula da sharar gida ta zamani, da kuma tsare-tsaren gine-ginen birane na zamani.
A ganawar, duk Bangarorin biyu sun amince da zurfafa haɗin kai a fannin fasaha da musayar ƙwarewa domin tallafawa sauyin jihar Kaduna zuwa tattalin arzikin mai ɗorewa.
Gwamna Sani ya bayyana cewa halartar Jihar Kaduna a taron (APCS 2025) na nuna shirin jihar na shiga sahun ƙasashen duniya wajen yin haɗin kai, ƙirƙira, da zama abin koyi a fannin ci gaba mai ɗorewa da ci gaban kowa da kowa a fadin Nijeriya da ma duniya baki ɗaya
ShareTweetSendShare MASU ALAKA