Aminiya:
2025-09-17@23:15:06 GMT

Chelsea ta kammala ɗaukar Garnacho daga Manchester United

Published: 31st, August 2025 GMT

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Chelsea ta tabbatar da ɗaukar ɗan wasan gaban Manchester United, Alejandro Garnacho, kan kuɗin da ya kai kusan fam miliyan 85 (£85m).

Rahotanni sun bayyana cewa ɗan wasan na ƙasar Argentina ya rattaba hannu kan kwantiragin zama a Stamford Bridge har zuwa shekarar 2032.

Hamas ta tabbatar da mutuwar jagoranta a Gaza, Mohammed Sinwar Xi na karɓar baƙuncin taron SCO a China

Garnacho, mai shekara 21, zai riƙa ɗaukar albashin fam 250,000 duk mako, kwatankwacin Naira miliyan 500 a kuɗin Nijeriya, lamarin ya sanya shi a sahun manyan ’yan wasa mafiya albashi a Stamford Bridge.

A bara ne tauraruwarsa ta haska a Manchester United, bayan ya ci ƙwallo 11 ya kuma ba da gudunmawar zura wasu 10 a raga.

A jimilla, ya buga wasanni 144 tun daga lokacin da aka ɗaukoshi daga Atlético Madrid a 2020, inda ya ci ƙwallo 26.

Ana iya tuna cewa Garnacho yana cikin ’yan wasa biyar da suka nemi barin United, ciki har da Marcus Rashford, Antony, Tyrell Malacia da Jadon Sancho, bayan wata matsala da ta shafi sabon tsarin koci a Old Trafford.

Kociyan Chelsea, Enzo Maresca, ya bayyana farin ciki da wannan cafane da aka yi, inda ya ce Garnacho zai ƙara wa ƙungiyar kuzari da saurin kai hare-haren a wasanninta.

“Ɗan wasa ne da yake iya sauya salon wasanni da kansa, kuma hakan zai taimaka wajen dawo da Chelsea cikin sahun manyan ƙungiyoyin masu neman kofuna,” in ji shi.

Masu sharhi sun ce wannan matakin zai ƙara armashi da zafi a gasar Premier League, musamman ganin yadda Garnacho ya saba taka rawar nuna kansa a manyan wasanni.

Sai dai da dama daga cikin magoya bayan Manchester United sun nuna takaicinsu kan cefanar da ɗan wasan da aka yi, inda suke ganin bai kamata a sayar da shi ba saboda a gina ƙungiyar da shi tare da sauran matasan ’yan wasan da ke nuna hazaƙa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Alejandro Garnacho Enzo Maresca

এছাড়াও পড়ুন:

An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar

Antoni Janar na Kotun Ɗaukaka Ƙara da ke birnin Yamai a Nijar, ya bayyana cewa an kama tsohon Ministan Harkokin Waje, Ibrahim Yacoubou, bisa zargin hannunsa a cikin wata aika-aika ta kisan kai domin yin tsafi.

A cewar Maazou Oumarou, lamarin ya samo asali ne daga wani binciken ’yan sanda da aka fara gudanarwa tun a ranar 29 ga Yuli, 2025.

KEDCO ya ƙaryata asibitin AKTH kan mutuwar majinyata saboda ɗauke wuta Dole sai mun tantance wa’azi kafin a yi —Gwamnan Neja

Ya bayyana cewa, an soma gudanar da binciken ne dangane da yunƙurin kisa a wani yanki da ke wajen birnin Yamai, lamarin da ya kai ga cafke ababen zargin a garin Dosso.

Wani mutum mai suna Mahamadou Noura ne ya bayyana cewa shi ne ya yi yunƙurin kisan, tare da wasu kashe-kashe guda shida da ya aiwatar a baya, bisa umarnin wasu mutane, ciki har da tsohon ministan Ibrahim Yacoubou.

Mutumin ya shaida wa mahukunta cewa ya aikata hakan ne domin yin tsafi da gawarwakin, a madadin wasu mutane da suka haɗa da: Issa Ali Maiga da Ismael Morou Karama da Elhadji Bilya da kuma Issa Seybou Hama.

TRT ya ruwaito cewa tuni dai an cafke duk ababen zargin, yayin da Kotun Ɗaukaka Ƙarar ta umurci ’yan sanda da su ci gaba da bincike tare da ɗaukar ƙarin matakan da za su tabbatar da gaskiya.

Sanarwar ta ce: “Manufar wannan mataki na shari’a ita ce a tattara cikakken rahoto da ke ƙunshe da dukkan abubuwan da suka faru, sannan a miƙa shi ga ɓangaren gurfanarwa.”

Mai shigar da ƙara a ɓangaren gwamnati ya ce, la’akari da girman wannan lamari, wajibi ne a gudanar da bincike cikin gaggawa.

Haka kuma ya buƙaci al’umma da su mutunta ’yancin kotu tare da bayar da cikakken goyon baya domin fayyace gaskiya.

Ana iya tuna cewa, Ibrahim Yacoubou na daga cikin manyan jami’an da aka kama bayan juyin mulkin Nijar na ranar 26 ga Yuli, 2023, sai dai daga bisani an ba shi beli na wucin gadi a cikin watannin baya.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Kammala Ziyarar Yini 3 A Ma’aikatar Kananan Hukumomin Jihar
  • An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
  • Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • Tawagar Yan Wasan Damben Gargajiya Ta Iran Ta Zama Zakara A Damben Ta Duniya
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara
  • Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara 
  • An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar
  • An kama mabaraci da kuɗaɗen ƙasar waje a Ilorin
  • Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff