Aminiya:
2025-11-02@12:27:42 GMT

Dangote ya ƙulla yarjejeniyar gina kamfanin taki na dala biliyan 2.5 a Habasha

Published: 29th, August 2025 GMT

Ƙasar Habasha ta rattaba hannu kan wata yarjejeniya da wani reshe na Rukunin Kamfanonin Dangote na Nijeriya domin gina wata sabuwar masana’antar samar da takin zamani na kimanin dala biliyan 2.5.

Hakan na ƙunshe cikin wani saƙo da Firayim Ministan Habasha, Abiy Ahmed ya wallafa a shafin X ranar Alhamis.

Sanusi Mikail Sami ya zama sabon Sarkin Zuru Babu ƙawancen da NNPP ta ƙulla da wata jam’iyyar — Kwankwaso

Abiy ya ce wannan yarjejeniya da Dangote Group na attajirin Afirka, Alhaji Aliko Dangote, za ta sanya ƙasarsa cikin jerin manyan ƙasashen da ke samar da takin zamani a duniya.

Ya bayyana cewa wannan aikin gina masana’antar wanda za a fara nan ba da jimawa ba, za ta riƙa samar da tan miliyan uku na takin zamani a kowace shekara.

“Wannan aikin zai samar da ayyukan yi ga ’yan ƙasa, ya tabbatar da wadatar takin zamani ga manomanmu da suka daɗe suna fama da ƙalubale.

“Sannan zai zama mataki na musamman a yunƙurinmu na cin gashin kai wajen samar da abinci,” in ji Abiy.

A watan Yuni, Aliko Dangote ya shaida cewa nahiyar Afirka za ta iya zama mai isar wa kanta da takin zamani cikin shekaru 40 bisa tsarin faɗaɗa masana’antarsa ta dala biliyan 2.5 da ke Legas.

A halin yanzu dai, Afirka na shigo da fiye da tan miliyan shida na takin zamani a kowace shekara, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ruwaito.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Ya Kamata Shugaba Tinubu Ya Ƙulla Alaƙa Ta Kut-da-kut Tsakanin Hukumar Shige Da Fice Da Kwastam – Babandede

“Iyakar kasa ba wai kawai yanki ne na tsaro ba. Yanki ne na al’adu; yanki ne na tarihi; haka nan ma yanki ne na tattalin arziki. Kula da shige da fice na da matukar amfani ga ci gabanmu. Wajibi ne Nijeriya ta zuba jari a kan kula da nau’in mutanen da take tacewa wajen shiga kasa da kuma irin mutanen da muke tacewa wajen fita daga kasa.

“Dole ne mu yi nazarin nau’in ayyukan da bakin-haure ke yi da kuma yadda suke shafar tattalin arzikinmu. Muna bukatar tsame mutanen da ke kawo cikas ga ci gabanmu”, in ji Babandede.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai Rundunar Sojin Nijeriya Ta Shirya Wa Janar Musa Faretin Gama Aiki October 31, 2025 Labarai Gwamnatin Tarayya Da Stellar Steel, Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Habaka Karafan Cikin Gida October 31, 2025 Labarai Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa October 31, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka
  • Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya
  • Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar
  • Sharrin son auren Mai Wushirya aka yi min — Mansura Isa
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Ya Kamata Shugaba Tinubu Ya Ƙulla Alaƙa Ta Kut-da-kut Tsakanin Hukumar Shige Da Fice Da Kwastam – Babandede
  • Real Madrid zata nemi diyyar Dala bilyan 4 daga UEFA
  • Gwamnatin Tarayya Da Stellar Steel, Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Habaka Karafan Cikin Gida
  • Borno ta fara fitar da kayan robobi zuwa ƙasashen waje – Zulum
  • Kamfanin Amazon na shirin sallamar ma’aikata 600,000 don maye gurbinsu da mutum-mutumi