Babu ƙawancen da NNPP ta ƙulla da wata jam’iyyar — Kwankwaso
Published: 29th, August 2025 GMT
Jagoran jam’iyyar NNPP a Nijeriya, Sanata Rabi’u Kwankwanso, ya ce suna jin daɗin jam’iyyarsu, kuma a halin da ake ciki babu wani ƙawance da suka ƙulla da wata jam’iyyar.
Yayin da yake jawabi a wajen taron majalisar ƙoli na jam’iyyar da aka gudanar a Abuja, Sanata Kwankwaso ya ce ba gaggawa suke yi ba.
Tsohon gwamnan na Kano ya ce kawo yanzu babu wata jam’iyya da suke tattaunawa da ita domin ƙulla ƙawance, sai dai ya ce hakan ba yana nufin ba za su tattauna da wata ba.
“’Yan jam’iyyarmu ba gaggawa suke yi ba, komai muna yinsa a hankali,” in ji shi.
“Muna da jam’iyyarmu [NNPP], kuma ba hanzari muke yi ba. Idan ana so a yi magana da mu babu matsala duk da ba mu manta da abin da aka yi mana a baya ba.
“Mu ’yan siyasa ne kuma a shirye muke mu tattauna da duk wanda ke son tattaunawa da mu.
“Har yanzu jam’iyyarmu na da rawar da za ta iya takawa a mulkin ƙasa,” in ji shi.
An dai jima ana raɗe-raɗin Kwankwaso zai koma jam’iyyar APC, tun bayan zaɓen 2023, inda har aka riƙa hasashen ba shi minista, lokacin da Shugaba Bola Tinubu ya ce zai yi aiki da ’yan hamayya a gwamnatinsa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Rabi u Musa Kwankwaso
এছাড়াও পড়ুন:
PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu da ke da alaƙa da Wike
Rikici a babbar jam’iyyar adawa ta PDP, na ƙara ƙamari, bayan da jam’iyyar ta dakatar da sakatarenta na ƙasa, Sanata Samuel Anyanwu, da wasu da ake ganin ’yan tsagin Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike ne.
Mai magana da yawun jam’iyyar na ƙasa, Debo Ologunagba ne, ya sanar da dakatarwar bayan wani taro da Kwamitin Ayyuka na Ƙasa (NWC), ya gudanar a hedikwatar jam’iyyar da ke Abuja.
Zargin Kisan Kiristoci: Maganar Trump a kan Najeriya tsagwaron ƙarya ce — Shehu Sani Zaɓen Tanzania: Shugaba Samia ta yi tazarce da kashi 97 an ƙuri’uSauran da aka dakatar sun haɗa da Mai Bai wa jam’iyyar Shawara kan Harkokin Shari’a, Kamaldeen Ajibade (SAN); Sakataren Tsara Harkokin Jam’iyya, Umar Bature; da Mataimakin Mai Bai wa jam’iyyar Shawara kan Harkokin Shari’a.
Rahotanni sun bayyana cewa waɗanda aka dakatar ba sa halartar tarukan jam’iyyar.
An dakatar da su na tsawon wata ɗaya, sannan aka miƙa lamarinsu ga Kwamitin Ladabtarwa na jam’iyyar PDP domin gudanar da bincike.
Waɗanda aka dakatar ’yan tsagin Wike ne, kuma sun raba ƙafa a rikicin da jam’iyyar ke fuskanta tun bayan zaɓen 2023.
Idan ba a manta ba, a ranar Juma’a ne, wata Babbar Kotu a Babban Birnin Tarayya, ta dakatar da PDP daga shirin gudanar da babban taronta da aka tsara yi a Ibadan, Jihar Oyo, a ranar 15 da 16 ga watan Nuwamba, 2025.
Sai dai jam’iyyar ta ce za ta ɗaukaka ƙara kan hukuncin, kuma hakan ba zai hana ta ci gaba da shirye-shiryen gudanar da taron ba.
Wasu daga cikin ’ya’yan jam’iyyar sun ce rashin jituwa a PDO shi ne babban dalilin da ya sa aka kai ƙarar taron’ kotu.