An kashe mutum 3 a faɗan ƙungiyoyin asiri a Legas
Published: 28th, August 2025 GMT
Aƙalla mutum uku ne sun rasu, yayin da wani ɗan sanda ya ji rauni a wani rikicin ƙungiyoyin asiri da ya auku a kasuwar Owode Onirin da ke Jihar Legas.
Rundunar ’yan sandan jihar, ta bayyana cewa tana neman Abiodun Ariori, Shugaban Kamfanin Golden Venture Limited, bisa zarginsa da hannu a rikicin.
HOTUNA: Tinubu ya dawo Abuja bayan ziyarar aiki a Japan da Brazil Kotu ta daure dan Shugaban Equatorial Guinea kan sayar da jirgin saman kasarShaidu sun ce ƙungiyoyin asirin biyu sun yi artabu da bindigogi, adduna da kwalabe.
Ɗan sandan da ya ji rauni an garzaya da shi asibiti, inda yake cikin mawuyacin hali.
Kakakin rundunar, CSP Benjamin Hundeyin, ya tabbatar da faruwar lamarin.
Amma ta ce komai ya daidaita tare da wanzar da zaman lafiya bayan da jami’an tsaro suka isa yankin.
Kwamishinan ’yan sandan jihar, CP Olohundare Jimoh, ya jagoranci tawagar ‘yan sanda zuwa kasuwar, inda suka buɗe hanyoyin da aka toshe yayin rikicin.
“A lokacin rikicin, mutane uku sun mutu a asibiti sakamakon raunukan da suka samu, yayin da wani ɗan sanda ɗaya ke cikin mawuyacin hali a asibiti,” in ji Hundeyin.
Rundunar ta kuma ƙaryata jita-jitar cewa rikicin ƙabilanci ne ya tashi a kasuwar Balogun.
Ta tabbatar da cewar faɗa ne tsakanin wasu ’yan daba, wanda ya yi sanadin mutuwar mutum ɗaya, kuma ba shi da alaƙa da ƙabilanci.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda Ɗan Sanda Faɗa kasuwa
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
Daga Usman Muhammad Zaria
Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta yi kira ga mazauna jihar Jigawa da su kasance masu bin doka da oda, tare da yin aiki kafada da kafada da rundunar ‘yan sanda domin tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali a fadin jihar.
Kwamishinan ‘Yan Sanda na jihar Jigawa, CP Dahiru Muhammad, ne ya bayyana haka lokacin da ya karɓi sabbin motoci 10 kirar Toyota Hilux da Gwamna Umar Namadi ya bai wa rundunar a Dutse, babban birnin jihar.
A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, SP Lawan Shiisu Adam, ya fitar, CP Dahiru Muhammad ya yaba da jajircewar Gwamna Umar Namadi wajen tallafa wa hukumomin tsaro domin sauke nauyin da ke kansu a jihar.
Ya bayyana cewa, wannan gudummawa ta nuna cikakken kudirin gwamnatin Gwamna Namadi na ƙara inganta harkokin tsaro da kuma tallafawa Rundunar ‘Yan Sanda ta Najeriya wajen aiwatar da aikinta na kare rayuka da dukiyoyin jama’a a fadin jihar.
Kwamishinan ya nuna cewa, waɗannan sabbin motoci 10 za su taimaka matuƙa wajen rage lokacin da ake ɗauka kafin amsa kiran gaggawa, tare da ƙara inganta aikin rundunar a fadin jihar.
Ya ƙara da cewa, za a yi amfani da motocin yadda ya kamata, tare da kula da su don tabbatar da ingantaccen tsaro.
CP Dahiru Muhammad ya kuma sake jaddada aniyar rundunar wajen ci gaba da tabbatar da zaman lafiya, doka da oda, tare da ƙarfafa haɗin gwiwa da sauran hukumomin tsaro da masu ruwa da tsaki.