Aminiya:
2025-09-17@21:51:10 GMT

An kashe mutum 3 a faɗan ƙungiyoyin asiri a Legas

Published: 28th, August 2025 GMT

Aƙalla mutum uku ne sun rasu, yayin da wani ɗan sanda ya ji rauni a wani rikicin ƙungiyoyin asiri da ya auku a kasuwar Owode Onirin da ke Jihar Legas.

Rundunar ’yan sandan jihar, ta bayyana cewa tana neman Abiodun Ariori, Shugaban Kamfanin Golden Venture Limited, bisa zarginsa da hannu a rikicin.

HOTUNA: Tinubu ya dawo Abuja bayan ziyarar aiki a Japan da Brazil Kotu ta daure dan Shugaban Equatorial Guinea kan sayar da jirgin saman kasar

Shaidu sun ce ƙungiyoyin asirin biyu sun yi artabu da bindigogi, adduna da kwalabe.

Ɗan sandan da ya ji rauni an garzaya da shi asibiti, inda yake cikin mawuyacin hali.

Kakakin rundunar, CSP Benjamin Hundeyin, ya tabbatar da faruwar lamarin.

Amma ta ce komai ya daidaita tare da wanzar da zaman lafiya bayan da jami’an tsaro suka isa yankin.

Kwamishinan ’yan sandan jihar, CP Olohundare Jimoh, ya jagoranci tawagar ‘yan sanda zuwa kasuwar, inda suka buɗe hanyoyin da aka toshe yayin rikicin.

“A lokacin rikicin, mutane uku sun mutu a asibiti sakamakon raunukan da suka samu, yayin da wani ɗan sanda ɗaya ke cikin mawuyacin hali a asibiti,” in ji Hundeyin.

Rundunar ta kuma ƙaryata jita-jitar cewa rikicin ƙabilanci ne ya tashi a kasuwar Balogun.

Ta tabbatar da cewar faɗa ne tsakanin wasu ’yan daba, wanda ya yi sanadin mutuwar mutum ɗaya, kuma ba shi da alaƙa da ƙabilanci.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Ɗan Sanda Faɗa kasuwa

এছাড়াও পড়ুন:

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
  • ‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja
  • Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
  • Kungiyar Kare Hakkokin Bil’Adama Ta Siriya Ta Bankado Karin Fararen Hula Da Aka Kashe A Rikicin Suweida
  • ’Yan sanda sun kama mutum 6 kan satar zinarin N109m a Kebbi
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 40 a masallaci a Zamfara
  • NDLEA ta kama ɗan Indiya da ƙwaya ta Naira biliyan 3 a Legas
  • ’Yan sanda sun sasanta rikicin asibitin AKTH da KEDCO