’Yan bindigar da suka sace ma’aurata a Katsina na neman N600m
Published: 28th, August 2025 GMT
’Yan bindigar da suka sace wani mutum, matarsa da ’yarsu a Jihar Katsina, na neman Naira miliyan 600 a matsayin kuɗin fansa.
Wanda aka sace sun haɗa da Anas Ahmadu mai shekara 33, matarsa Halimat, da kuma ’yarsu Jidda.
Ba zan tsaya takarar kowanne irin mukami ba a 2027 – El-Rufai NAJERIYA A YAU: Matakan da ciwon suga ke bi kafin illata mai fama da shiAn sace su ne a gidajensu da ke Filin Canada Quarters a Sabuwar Unguwa, cikin garin Katsina da safiyar ranar Talata.
A yayin kai harin, wani ɗan sa-kai mai shekara 25 mai suna Abdullahi Muhammad, ya rasu lokacin da yake ƙoƙarin ceto su.
Wani ɗan uwan ma’auratan ya shaida wa Aminiya cewa ’yan bindigar sun kira ɗan uwan Halimat, Malam Ibrahim, ta wayar Anas domin neman kudin fansa Naira Miliyan 600.
Sai dai iyalan sun bayyana cewa ba za su iya biyan wannan kuɗi ba.
Radda ya dawo daga hutu saboda hare-haren ’yan bindiga a KatsinaGwamnan Jihar Katsina, Dikko Umar Radda, ya dawo daga hutun jinyar da yake yi a ƙasashen waje, sakamakon sabbin hare-haren ’yan bindiga a jihar.
A ranar Laraba, gwamnan ya kai ziyara ta’aziyya ƙauyen Gidan Mantau, a Karamar Hukumar Malumfashi, inda ’yan bindiga suka kashe masallata a wani masallaci a ranar 19 ga watan Agusta.
Shaidu sun ce harin ya auku ne a lokacin da jama’a ke yin sallar Asuba.
Rahotanni sun nuna cewa maharan sun kai harin ne a matsayin ramuwar gayya, bayan da mutanen yankin suka yi musu kwanton-ɓauna, tare da kashe mutanensu sannan suka ƙwace musu makamai da babura.
Hakazalika, an ruwaito cewa ’yan bindigar sun ƙone sama da mutum 20 a gidajensu lokacin da suka sake kai hari Gidan Adamu Mantau, a Unguwar Yar Mai Dabo, Makera da kuma Burdigau.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga hare hare Ma aurata Radda yan bindigar
এছাড়াও পড়ুন:
Araqchi: Da Hadin Bakin Amurka, Gwamnatin Isra’ila ta kaddamar Da Hari Kan Kasar Iran
Ministan harkokin wajen Iran ya jaddada cewa: Isra’ila ba za ta kai hari kan Iran ba sai da goyon bayan Amurka
Ministan harkokin wajen Iran Seyyed Abbas Araqchi ya bayyana cewa: Gwamnatin ‘yan sahayoniyya ba za ta kaddamar da yaki kan Jamhuriyar Musulunci ba tare da samun wata kariya daga Amurka ba. Ya kara da cewa, Iran ta gudanar da yakin kwanaki goma sha biyu da wannan gwamnati mai wuce gona da iri, kuma ta hana ta ci gaba da mummunar manufarta ta mamaya a yankin.
A wata hira da ya yi da gidan talabijin na Al- Jazeera, Araqchi ya yi nuni da cewa: Gwamnatin masu wuce gona da iri ta yi kokarin fadada yakin zuwa yankin ta hanyar kai hari kan cibiyoyin man fetur na Iran, amma Iran ta yi nasarar shawo kan yakin kuma ta hana aukuwan hakan.”
Yayin da yake fayyace shirye-shiryen Jamhuriyar Musulunci ta Iran na tattaunawa don kawar da damuwar da ake da ita game da shirin makamashin nukiliyarta na zaman lafiya, Ministan Harkokin Wajen ya jaddada cewa: “Sun shirya wa duk wani abu da zai faru kuma suna tsammanin duk wani hali mai tsauri daga ‘yan sahayoniyya.” Ya bayyana cewa Iran ta samu kwarewa mai yawa daga yakin da ta yi kwanan nan kuma ta samu damar gwada makamai masu linzaminta a wannan yaƙi na gaske.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Larijani: Iran Ba Ta Tsoron Gudanar Da Tattaunawa, Amma Ta Zama Mai Amfani November 2, 2025 Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza November 2, 2025 Kasar Qatar Ta Ba Da Tallafin Gaggawa Ga Al’ummar Sudan Bayan Gumurzun El-Fasher November 2, 2025 IAEA : Babu wata shaida da ke nuna cewa Iran na kera makaman nukiliya November 2, 2025 Amurka : zamu dauki matakin soja idan Najeriya ta gaza kawo karshen kashe Kiristoci November 2, 2025 Hamas ta musanta zargin Amurka na cewa tana sace kayan agaji a Gaza November 2, 2025 Wasu Yan Ta’adda Sun Kashe Dakarun Sa Kai 2 A Kudu Maso Gabashin Iran November 2, 2025 Sojojin Amurka Na Kara Fuskantar Venezuwela Adaidai Lokacin da Trump Ke Musanta Batun Kai Hari November 2, 2025 Isra’ila Ta Kashe Mutane 4 Tare Da Jikkata Wasu Guda 3 A Kudancin Labanon November 2, 2025 Iran Ta Gargadi Isra’ila Kuma Tasha Alwashin Kare Shirinta Na Nukiliya November 2, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci