Sabon fira ministan kasar Sudan Kamil Idris ya yi kira ga kasashen waje masu taimaka wa dakarun daukin gaggawa “RSF” da su kawo karshen taimakon da suke bawa masu aikata laifi.”

Idris wanda yake jawabin bayan kama aiki a jiya ya ce; Jami’an tsaro da kuma mahukuntan kasar ta Sudan suna da cikakken goyon baya a kasar don kawo karsehn ‘yan tawaye, masu dauke da makamai.

Idris ya kuma ce; A shirye yake ya yi wa kasa aiki a cikin kekyawar anniyya da kwazo.”

Gwamantin kasar Sudan dai tana zargin Hadaddiyar Daular Larabawa da taimaka wa dakarun kai daukin gaggawa “RFS” wacce ta dauki shekaru biyu tana fafatawa da sojojin kasar.

Wasu daga cikin  kasashen da Sudan take  zargi da hannu a tawayen na “RSF” sun hada da Chadi, Libya da Sudan Ta Kudu.

Wasu rahotannin suna nuni da cewa, suna bawa wannan kungiyar makamai ne ta kan iyakokin da su ka hada wadannan kasashe da Sudan.

Tun barkewar yakin basasa a kasar Sudan a ranar 15 ga watan April 2023, zuwa yanzu adadin mutanen da su ka rasa rayukansu sun kai 24,000, yayin da wasu fiye da miliyan 14 su ka zama ‘yan gudun gijira, miliyan 4 daga cikinsu sun fice daga kasar, zuwa kasashen makwabta.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Araghchi zai fara ziyarar kwanaki biyu a kasashen Masar da Lebanon

A wani lokaci yau Litini ne ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi zai fara ziyarar kwanaki biyu a kasashen Masar da Lebanon.

Yayin ziyarar Araghchi zai gana da manyan jami’an Masar da na Lebanon domin tattauna dangantakar da ke tsakanin kasashen biyu dama rikicin yankin.

Ziyarar Araghchi a Masar za ta gudana ne bisa gayyatar takwaransa na Masar Badr Abdelatty.

Ana sa ran ministan harkokin wajen na Iran zai gana da shugaban Masar Abdel Fattah al-Sisi, da takwaransa Badr Abdelatty, da kuma wasu masu fada a ji a fannin tattalin arzikin Masar.

Da yake karin haske kan manufar ziyarar, mai kula da harkokin Iran a Alkahira ya ce, rikice-rikicen yankin da suka hada da hare-haren wuce gona da iri na Isra’ila a Gaza da kuma rikicin Sudan da Libya, na daga cikin batutuwan da bangarorin zasu musayar ra’ayi .

Dangane da alakar da ke tsakanin Tehran da Alkahira, ya ce ana ci gaba da samun ci gaba, tare da tuntubar juna da tattaunawa mai zurfi tsakanin ministocin harkokin wajen kasashen biyu.

Ya ce yana fatan Iran da Masar za su dauki mataki na karshe don kyautata alakarsu nan gaba kadan. Ban da haka kuma, Iran tana goyon bayan adawar Masar na tilastawa ‘yan Gaza gudun hijira.

A watan Disamba na shekarar 2024, shugaban kasar Iran Massoud Pezechkian ya ziyarci Masar, ziyarar farko da shugaban kasar Iran ya kai kasar Larabawar tun shekara ta 2013.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Kasar Iran Ya Jaddada Cewa: Amurka Da Isra’ila Suna Da Mugun Nufi Kan Iran Da Kasashen Musulmi
  • Iran ta bukaci hadin kan al’ummar Lebanon wajen warware matsalolin kasar
  • Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Ondo Da Shugaban Masu Rinjaye Sun Yi Murabus
  • Ana samun Karancin Masu Sayen Dabbobi A Kano Duk Karatowar Sallar Layya
  • Sabon Firay Ministan Sudan Ya Bukaci Kasashen Dake Taimaka Wa “RSF” Da Su Daina
  • Arakci: Cinikayya A Tsakanin Iran Da Masar Za Ta Kara Bunkasa
  • Fira Ministan Kasar Senegal Yana Ziyarar Aiki A Kasashen Yammacin Afirka
  • Kasar Iran Ta Soki Rahoton Hukumar IAEA Na Baya-Bayan Nan Shirinta Na Makamashin Nukiliya
  • Araghchi zai fara ziyarar kwanaki biyu a kasashen Masar da Lebanon