Sahun ƙarshe na mahajjata 140 daga jihar Kwara, ciki har da jami’an NAHCON, da ya tashi daga filin jirgin sama na Babatunde Idiagbon da ke Ilori ya isa kasar Saudiyya domin gudanar da aikin Hajjin shekarar 2025.

Yayin jawabi ga mahajjatan kafin tashin su da misalin ƙarfe 6:42 na yammacin Laraba, Shugaban Hukumar Jin Daɗin Alhazai na Jihar Kwara, Farfesa Mashood Mahmud-Jimba, ya shawarci mahajjatan da su kasance masu ɗabi’a a lokacin da suke kasa mai tsarki.

Farfesa Mahmud-Jimba ya bayyana cewa an shirya duk abin da ya dace domin tabbatar da cewa mahajjatan sun gudanar da aikin hajji ba tare da wata matsala ba.

Ya kuma shawarce su da kada su yi ayyuka masu wahala domin samun damar shiryawa yadda ya kamata don gudanar da ibadarsu.

Shugaban ya kuma ja hankalinsu da su yi amfani da cibiyoyin lafiya da aka samar idan suna buƙatar magani.

A nasa jawabin, Amirul Hajj na Jihar Kwara na shekarar 2025, kuma Olupo na Ajase-Ipo, Barista Ismail Yahaya-Alebiosu, ya bayyana jin daɗinsa da irin shirin da aka yi domin jigilar mahajjatan zuwa Saudiyya.

Ya yaba wa gwamnan jihar bisa bayar da goyon baya da kayayyakin aiki ga hukumar domin tabbatar da gudanar da aikin hajji ba tare da tangarda ba.

Barista Yahaya-Alebiosu ya kuma shawarci mahajjatan da su kiyaye dokoki da ƙa’idodi yayin da suke kasa mai tsarki.

A nasa bangaren, Sakataren zartarwa na Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kwara, Alhaji Abdulsalam Abdulkadir, ya shawarci mahajjatan da su zama jakadun ƙasa nagari.

Ya kuma bukace su da su yi addu’a domin zaman lafiya da ci gaban tattalin arzikin ƙasa yayin da suke a kasa mai tsarki.

Jimillar mahajjata 2,210 daga jihar Kwara ne ake sa ran za su gudanar da aikin Hajjin shekarar 2025.

 

Ali Muhammad Rabi’u

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: gudanar da aikin Jihar Kwara

এছাড়াও পড়ুন:

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

Hukumar NDLEA ta bayyana cewa wata ƙungiyar masu safarar miyagun ƙwayoyi ce a filin jirgin sama na Kano ta boye jakunkunan ƙwayoyi a cikin kayan matafiyan.

An kama shugaban ƙungiyar, Ali Abubakar Mohammed (wanda aka fi sani da Bello Karama), tare da wasu abokan aikinsa.

Hukumar ta ce mutanen ukun ba su da laifi kuma an zalunce su ne kawai.

An saki su ne bayan bincike da kuma ƙoƙarin diflomasiyya na tsawon makonni.

Lamarin ya tayar da hankali kan tsaro a filayen jirgin sama a Nijeriya da yadda masu aikata laifuka ke amfani da fasinjoji marasa laifi.

Hukumar ta ce za a ɗauki ƙarin matakai don hana faruwar irin wannan lamari.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Karamar Hukumar Malam Madori Ta Horar Da Mata Kare Kai Daga Cututtukan Mahaifa
  • Kwara ETF Ya Dauki Nauyin Karatun Fitattun Dalibai A Matakin Sakandare
  • An tattauna yadda za a inganta walwalar malamai a Gombe
  • Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
  • Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo
  • ALGON ta karrama Gwamna Buni da lambar yabo kan kawo ci gaba a Yobe
  • NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba
  • Ɗangote zai gina ɗakunan kwanan ɗalibai 250  a Jami’ar Ilorin
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa