Jirgin Karshe Na Alhazan Jihar Kwara Ya Isa Kasa Mai Tsarki
Published: 22nd, May 2025 GMT
Sahun ƙarshe na mahajjata 140 daga jihar Kwara, ciki har da jami’an NAHCON, da ya tashi daga filin jirgin sama na Babatunde Idiagbon da ke Ilori ya isa kasar Saudiyya domin gudanar da aikin Hajjin shekarar 2025.
Yayin jawabi ga mahajjatan kafin tashin su da misalin ƙarfe 6:42 na yammacin Laraba, Shugaban Hukumar Jin Daɗin Alhazai na Jihar Kwara, Farfesa Mashood Mahmud-Jimba, ya shawarci mahajjatan da su kasance masu ɗabi’a a lokacin da suke kasa mai tsarki.
Farfesa Mahmud-Jimba ya bayyana cewa an shirya duk abin da ya dace domin tabbatar da cewa mahajjatan sun gudanar da aikin hajji ba tare da wata matsala ba.
Ya kuma shawarce su da kada su yi ayyuka masu wahala domin samun damar shiryawa yadda ya kamata don gudanar da ibadarsu.
Shugaban ya kuma ja hankalinsu da su yi amfani da cibiyoyin lafiya da aka samar idan suna buƙatar magani.
A nasa jawabin, Amirul Hajj na Jihar Kwara na shekarar 2025, kuma Olupo na Ajase-Ipo, Barista Ismail Yahaya-Alebiosu, ya bayyana jin daɗinsa da irin shirin da aka yi domin jigilar mahajjatan zuwa Saudiyya.
Ya yaba wa gwamnan jihar bisa bayar da goyon baya da kayayyakin aiki ga hukumar domin tabbatar da gudanar da aikin hajji ba tare da tangarda ba.
Barista Yahaya-Alebiosu ya kuma shawarci mahajjatan da su kiyaye dokoki da ƙa’idodi yayin da suke kasa mai tsarki.
A nasa bangaren, Sakataren zartarwa na Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kwara, Alhaji Abdulsalam Abdulkadir, ya shawarci mahajjatan da su zama jakadun ƙasa nagari.
Ya kuma bukace su da su yi addu’a domin zaman lafiya da ci gaban tattalin arzikin ƙasa yayin da suke a kasa mai tsarki.
Jimillar mahajjata 2,210 daga jihar Kwara ne ake sa ran za su gudanar da aikin Hajjin shekarar 2025.
Ali Muhammad Rabi’u
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: gudanar da aikin Jihar Kwara
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai
Gwamnatin Jihar Yobe ta ƙaddamar da shirin fara amfani da ma’adinan ƙarƙashin ƙasa da Allah SWT ya hore ma ta da nufin haɓaka tattalin arzikinta tare da samarwa al’umma aikin yi.
A yayin ƙaddamar da taron masu ruwa da tsaki na Jihar da aka yi a babban ɗakin taron gidan gwamnatin Jihar da ke Damaturu, Gwamnan Jihar Mai Mala Buni ya ce kamfanin haɓaka ma’adanai ta Yobe Limited ita ce kawai hukumar da aka bai wa izini don gudanar da duk ayyukan bincike da haƙar ma’adinai a faɗin jihar.
Kotu ta dakatar da babban taron PDP na ƙasa Real Madrid zata nemi diyyar Dala bilyan 4 daga UEFAYana mai cewa, kamfanin haƙar ma’adinai na Yobe a halin yanzu shi ne, ƙashin bayan da zai samarwa Jihar hanyoyin dogaro.
“Jihar Yobe tana da wadataccen albarkatun ma’adinai kamar: Limestone, gypsum, kaolin, granite, Quartz, silica da sauran su duk da haka, tsawon shekaru da yawa, waɗannan ma’adinai sun kasance ba a amfani da su sosai kuma a yanzu lokaci ya yi da za a mayar da waɗannan ma’adinai da aka ɓoye zuwa kadarorin da za su samar da ayyukan yi, samar da wadata da kuma ciyar da ci gaban zamantakewa da tattalin arziki na mutanenmu gaba ɗaya.”
“Manufarmu ita ce tsara wani tsari don ci gaban fannin haƙar ma’adinai a Jihar Yobe ta hanyar da ta dace da manufofin Gwamnatin Tarayya na tabbatar da haɗa kan al’umma, jawo hankalin masu zuba jari masu aminci da kuma tabbatar da alhakin gyara muhalli.
“kuma mun yi imanin cewa haƙar ma’adinai idan aka sarrafa shi yadda ya kamata, zai iya zama babban abin da ke haifar da juriyar tattalin arzikin jiharmu, samar da aikin yi ga matasa da kuma samar da kuɗaɗen shiga.”
“Muna hasashen samar da fannin haƙar ma’adinai wanda zai iya aiki a cikin tsarin dokoki, wanda ke tabbatar da ɗorewar muhalli da fa’idar al’umma; wanda ke haɗaka da haɗin gwiwar gwamnati da masu zaman kansu waɗanda aka amince da riƙon amana; wanda ke jawo hankalin masu zuba jari na ƙasashen waje.” Cewar Gwamna Buni.