Aminiya:
2025-11-02@20:54:38 GMT

Gwamnati za ta sayar da gidaje 753 da EFCC ta ƙwato a hannun Emefiele 

Published: 21st, May 2025 GMT

Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa za ta sayar da gidaje 753 da aka ƙwato daga tsohon gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN), Godwin Emefiele.

Wannan sanarwar ta fito ne daga Ministan Gidaje, Ahmed Dangiwa, a ranar Talata yayin da yake karɓar takardun mallakar gidajen daga hannun Hukumar EFCC.

Mun dakatar da sanya tallan magungunan gargajiya a fina-finai – Abba ’Yan sanda sun cafke ’yan fashi 6, sun ƙwato motocin sata 4 a Kano

Gidajen suna cikin Babban Birnin Tarayya, Abuja.

Ministan, ya gode wa EFCC saboda yadda ta ke aiki tuƙuru wajen yaƙar cin hanci da rashawa.

A cewar sanarwar da kakakin ma’aikatar, Salisu Haiba, ya fitar, an tabbatar cewa waɗannan kadarori na daga cikin dukiyoyin da aka ƙwato daga hannun masu almundahana da kuɗaɗen jama’a.

Idan ba a manta ba Emefiele na ci gaba da fuskantar tuhume-tuhume da suka shafi cin hanci da rashawa, tun bayan sauke shi daga shugabancin CBN.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan bindiga sun sace fasinjoji a cikin motocin bas a Kogi

Wasu ’yan bindiga da ake zargin masu garkuwa da mutane ne sun yi garkuwa da fasinjoji a cikin wasu motocin bas Toyota guda biyu a titin Itobe zuwa Ajegwu-Anyigba a Ƙaramar hukumar Ofu ta jihar Kogi.

An samu rahoton cewa, lamarin ya faru ne a ranar Alhamis da misalin ƙarfe 5 na asubahi a tsakanin ƙauyukan Ojiwo’-Ajengo da Mamereboh da ke kan babbar hanyar.

Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai Kotu ta dakatar da babban taron PDP na ƙasa

An ce masu garkuwa da mutanen sun yi amfani da wata tirela da aka kama wajen tare hanyar bayan shingen binciken jami’an tsaro, da ke kusa da wurin da lamarin ya faru.

Shedun gani da ido sun ce ɗaya daga cikin motocin bas ɗin mai lamba KG: KPA 622LG na kan hanyarta zuwa Abuja, tare da fasinjoji daga wata tashar mota a unguwar Ankpa da ke yankin Kogi ta Gabas.

Har yanzu ba a iya gano adadin fasinjojin da aka yi garkuwa da su ba zuwa yanzu, sai dai mun iya tabbatar da cewa ɗaya daga cikin motocin na ɗauke da fasinjoji ne daga yankin Ankpa, kamar yadda aka gano wasu takardu da wasu kayayyaki a wurin da lamarin ya faru suka bayyana.

“Motocin bas ɗin guda biyu suna kan hanyar Abuja ne a lokacin da suka ci karo da shingayen ’yan bindiga a safiyar ranar Alhamis. Dukkanin fasinjojin, ciki har da direban motocin bas ɗin biyu an yi awon gaba da su cikin daji,” in ji Unubi Ademu, wani mazaunin Achigili, a ƙauyen da ke maƙwabta.

Al’ummar yankin sun ƙara da cewa, jami’an tsaro da suka haɗa da sojoji da mafarauta da kuma ’yan banga suna ƙoƙarin magance lamarin.

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan Jihar Kogi (PPRO), CSP William Aya bai amsa kira da saƙo ba lokacin da aka tuntuɓe shi har zuwa lokacin tattatara wannan rahoto.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba
  • Kisan Kiristoci: Lauyoyi sun nemi Gwamnatin Tarayya ta tattauna da Amurka
  • An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3
  • Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • ’Yan bindiga sun sace fasinjoji a cikin motocin bas a Kogi
  • Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar
  • Gwamnatin Tarayya Da Stellar Steel, Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Habaka Karafan Cikin Gida
  • Madagascar Ta Sanar da Kafa Sabuwar Gwamnati Tare da Manyan ‘Yan Adawa
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Daliban Makarantar Kudi Suka Fi Na Gwamnati Kokari