Aminiya:
2025-07-05@07:28:06 GMT

Gwamnati za ta sayar da gidaje 753 da EFCC ta ƙwato a hannun Emefiele 

Published: 21st, May 2025 GMT

Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa za ta sayar da gidaje 753 da aka ƙwato daga tsohon gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN), Godwin Emefiele.

Wannan sanarwar ta fito ne daga Ministan Gidaje, Ahmed Dangiwa, a ranar Talata yayin da yake karɓar takardun mallakar gidajen daga hannun Hukumar EFCC.

Mun dakatar da sanya tallan magungunan gargajiya a fina-finai – Abba ’Yan sanda sun cafke ’yan fashi 6, sun ƙwato motocin sata 4 a Kano

Gidajen suna cikin Babban Birnin Tarayya, Abuja.

Ministan, ya gode wa EFCC saboda yadda ta ke aiki tuƙuru wajen yaƙar cin hanci da rashawa.

A cewar sanarwar da kakakin ma’aikatar, Salisu Haiba, ya fitar, an tabbatar cewa waɗannan kadarori na daga cikin dukiyoyin da aka ƙwato daga hannun masu almundahana da kuɗaɗen jama’a.

Idan ba a manta ba Emefiele na ci gaba da fuskantar tuhume-tuhume da suka shafi cin hanci da rashawa, tun bayan sauke shi daga shugabancin CBN.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Nijeriya Na Kewar Gwamnatin Buhari Saboda Azabar Da Suke Fuskanta A Hannun Tinubu – Amaechi

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yan Kasuwa Na Kalubalantar Rage Faranshin Man Dangote
  • Shugaban Kasar Iran Ya Gana Da Fira Ministan Pakistan Tare Da Tattaunawa Kan Harin Da Iran Ta Fsukanta
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda da ƙwato makamai a Borno
  • ‘Yan Nijeriya Na Kewar Buhari Saboda Azabar Da Suke Fuskanta A Hannun Tinubu – Amaechi
  • ‘Yan Nijeriya Na Kewar Gwamnatin Buhari Saboda Azabar Da Suke Fuskanta A Hannun Tinubu – Amaechi
  • Filato: Mahara sun cire hannun matashi a kan hanyar komawa gida daga jana’iza
  • Ambaliya da iska sun rushe gidaje 171 a watanni biyu a Gombe – SEMA
  • ’Yan Najeriya sun fara begen Buhari saboda azabar Tinubu – Amaechi
  • ’Yan Najeriya sun fara begen Buhari saboda azabar TIinubu – Amaechi
  • Iraki Ta Kai Karar HKI Kan Amfani Da Sararin Samaniyar Kasar Don Kaiwa Iran Hare hare