Aminiya:
2025-05-21@02:37:34 GMT

Gwamnati za ta sayar da gidaje 753 da EFCC ta ƙwato a hannun Emefiele 

Published: 21st, May 2025 GMT

Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa za ta sayar da gidaje 753 da aka ƙwato daga tsohon gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN), Godwin Emefiele.

Wannan sanarwar ta fito ne daga Ministan Gidaje, Ahmed Dangiwa, a ranar Talata yayin da yake karɓar takardun mallakar gidajen daga hannun Hukumar EFCC.

Mun dakatar da sanya tallan magungunan gargajiya a fina-finai – Abba ’Yan sanda sun cafke ’yan fashi 6, sun ƙwato motocin sata 4 a Kano

Gidajen suna cikin Babban Birnin Tarayya, Abuja.

Ministan, ya gode wa EFCC saboda yadda ta ke aiki tuƙuru wajen yaƙar cin hanci da rashawa.

A cewar sanarwar da kakakin ma’aikatar, Salisu Haiba, ya fitar, an tabbatar cewa waɗannan kadarori na daga cikin dukiyoyin da aka ƙwato daga hannun masu almundahana da kuɗaɗen jama’a.

Idan ba a manta ba Emefiele na ci gaba da fuskantar tuhume-tuhume da suka shafi cin hanci da rashawa, tun bayan sauke shi daga shugabancin CBN.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Mawaƙan APC sun zargi gwamnatin Jigawa da yin watsi da su

Wasu mawaƙan jam’iyyar APC da ke Jihar Jigawa, sun bayyana ɓacin ransu kan yadda gwamnatin jihar ta yi watsi da su, duk da irin gudunmawar da suka bayar wajen samun nasarar jam’iyyar a zaɓen 2023.

Mawaƙan wajen su 35, sun gudanar da wani taro, inda suka bayyana damuwarsu da kuma sanar da cewa sun janye daga duk wata hulɗa da gwamnatin jihar, har sai an ba su kulawar da ta dace.

Hajji: Gwamnan Gombe ya yi bankwana da maniyyata 966, ya bai wa kowa kyautar Riyal 200 NAJERIYA A YAU: Mece ce Makomar Dimokuraɗiyya Idan Aka Wajabta Kada Kuri’a?

Shugaban mawaƙan jihar, Lawan Gujungu Mai Babban Gandu ne, ya jagoranci taron, inda ya shaida wa manema labarai cewa tun bayan da sabon gwamnan ya hau mulki sama shekara biyu, har yanzu ba su sharɓi romon dimokuraɗiyya ba.

Ya ce mawaƙan sun yi haƙuri na tsawon lokaci suna sa ran za a saka musu, amma abin ya gagara.

A cewarsa: “Mun shiga mawuyacin hali. Muna cikin APC tun asali, mun yi wa jam’iyya hidima sosai a lokacin yaƙin neman zaɓe, mun ƙirƙiri waƙoƙi da dama don tallata manufofin jam’iyyar da kwatanta cancantar ’yan takararta.

“Amma yanzu da muka ci zaɓe kuma muka kafa gwamnati, an watsar da mu tamkar ba mu da wata ƙima.”

Lawan, ya ƙara da cewa daga yanzu mawaƙan za su nisanci duk wani taro ko aikin da ya shafi gwamnati, har sai an saurare su tare da mutunta su da irin gudunmawar da suka bayar.

Wannan bore ya fito fili ne a daidai lokacin da ake buƙatar jituwa da haɗin kai tsakanin masu ruwa da tsaki a cikin jam’iyyar da kuma gwamnatin jihar domin ci gaban al’umma.

Wasu daga cikin mawaƙan da suka halarci taron sun bayyana cewa suna fatan gwamnan zai ji ƙorafinsu kuma ya ɗauki matakin da ya dace, domin ci gaba da gina jam’iyya da gwamnatin da kowa ke alfahari da ita.

Tuni dai wannan batu ya jawo ce-ce-ku-ce a cikin jam’iyyar APC a Jihar Jigawa, inda wasu ke ganin cewa ya kamata gwamnati ta sake duba rawar da waɗanda suka ba da gudunmawa kafin kafa gwamnati, domin gudun fuskantar tawaye.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • EFCC Ta Miƙa Gidaje 750 Na Emefiele Da Ta Ƙwace Ga Ministan Gidaje
  • ’Yan sanda sun cafke ’yan fashi 6, sun ƙwato motocin sata 4 a Kano
  • Shugaba Kasar Lebanon Ya Ce Kungiyar Hizbullah Bata Da Zabi Sai Abinda Gwamnati Ta fada
  • Zulum ya roƙi Gwamnatin Tarayya ta kai wa Marte ɗauki
  • Mawaƙan APC sun zargi gwamnatin Jigawa da yin watsi da su
  • Fira Ministan Libiya Ya Tantance Bangarorin Da Kula Da Hakkin Tsaron Kasar Ya Rataya A Wuyarsu
  • Sojoji Sun Kashe Na Hannun Daman Bello Turji A Sokoto
  • Zargin Kin Amincewar Kwankwaso Zuwa APC: Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Mai Taimaka Ma Ta
  • Senegal ta karbi wani sansaninta na uku daga hannun Faransa