Gwamnatin jihar Zamfara ta bayyana cewa babu wani kamfen batanci da zai hana Gwamna Dauda Lawal aiwatar da ayyukan da suka shafi al’umma a fadin jihar.

 

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da babban daraktan yada labarai da sadarwa na gwamna, Malam Salihu Nuhu Anka ya rabawa manema labarai a Gusau.

 

A cewar Anka, Gwamna Lawal ya fara aiki ne a wani aikin ceto, kuma tuni mazauna jihar suka fara cin ribar dimokuradiyya.

 

Ya bayyana cewa hankalinsa ya karkata ne kan kalaman da ya bayyana a matsayin maras tushe da wani tsohon Kwamishinan Yada Labarai, Ibrahim Magaji Dosara ya yi, yayin wani taron manema labarai a Kaduna, inda ya kalubalanci kalaman da Gwamna Lawal ya yi a wata hira da ya yi da shi kwanan nan.

 

“A yayin taron manema labarai, Dosara ya kai wa Gwamna Dauda Lawal hari cikin rashin kunya a kokarinsa na burge tsohon Gwamna Bello Matawalle,” Anka ya yi zargin.

 

 

REL/AMINU DALHATU.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Dosara Zamfara

এছাড়াও পড়ুন:

Isra’ila ta hana ayarin motocin agaji na arewacin Afrika shiga Gaza

Ministan yakin Isra’ila, Israel Katz, ya umarci sojojin kasar da su hana ayarin motocin agaji na arewacin Afirka shiga yankin Zirin Gaza da aka yi wa kawanya.

A cikin wata sanarwa ofishin Katz ya umarci sojojin Isra’ila da su hana “masu fafatuka daga Masar shiga yankin Zirin Gaza.

Katz bukaci “Hukumomin Masar dasu hana zuwan masu fafatukar a kan iyakar Masar da Isra’ila.”

Ministan ya ya bayyana hakan a matsayin hadari ga jami’an tsaron Isra’ila na IDF.”

Wannan dai na zuwa ne bayan ayarin motoci 100 da ya kunshi dubban masu fafatuka daga kasashen Morocco, Aljeriya, Tunisia, Libya da Masar, suka yunkuri anniyar wayar da kan al’ummar duniya kan matsalar jin kai a Gaza, da neman kawo karshen yakin kisan kare dangi, da karya shingen da Isra’ila ke yi da kuma kai muhimman kayayyakin jin kai a Gaza.

Ayarin da ya kunshi kungiyoyin kwadago da masu fafutukar kare hakkin bil’adama da ‘yan wasa da lauyoyi da likitoci da ‘yan jarida da na kungiyoyin matasa da dai sauransu ana sa ran za su shiga Masar a yau Alhamis kafin isa mashigar Rafah da ke kan iyaka a kudancin zirin Gaza.

Kafin hakan dama sojojin Isra’ila sun kwace jirgin ruwan agaji na Madleen da ke kan hanyarsa ta zuwa Gaza domin kai tallafi ga al’ummar Zirin, bayan shafe sama da watanni ashirin na yakin kisan kare dangi da Isra’ila ke yi.

An kama dukkan masu fafutukar na kasa da kasa su 12 da ke cikin jirgin, ciki har da mai fafutukar Sweden Greta Thunberg.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An samu gobara a wasu matatun mai guda biyu na Iran bayan harin da Isra’ila ta kai
  • Wutar lantarki ta kashe mutum 5, ta jikkata 13 a Gombe
  • Arakci: Babu Wani Dalili Na Ci Gaba Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka
  • Wutar Lantarki Mai Ƙarfi Ta Yi Ajalin Mutum Biyar A Gombe
  • Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025
  • Bin Hanya Daya Da Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Muhimmin Mataki Ne Na Ba Da Tabbaci Ga Huldar Ciniki Da Tattalin Arzikin Sin Da Amurka
  • Kamfanonin Waje Sun Ce Dole Ne Su Shiga A Dama Da Su A Cikin Kasuwar Kasar Sin
  • Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6
  • Isra’ila ta hana ayarin motocin agaji na arewacin Afrika shiga Gaza
  • An hana hawa babur da daddare a fadin jihar Gombe