Bankin Zenith Ya Samu Ribar Naira Tiriliyan 3.97
Published: 19th, April 2025 GMT
Wannan nasarar ta nona irin namijin kokarinda Bankin ya yi na kara habaka samar wa da kansa kudaden shiga duk da matsin tattalin arzikin da kasar nan ke fuskanta.
Bugu da kari, kadarorin Bankin sun karu zuwa jimmlar kaso 47 daga Naira tiriliyan 20 a shekarar 2023 zuwa Naira tiriliyan 30, a shekarar 2024.
Kazalika, abokan huddar Bankin sun karu zuwa kashi 45, wanda kudaden da suka ajiyarsu ya karu zuwa Naira tiriliyan 22 a shekarar 2024, sabanin yadda ya ke kan Naira tiriliyan 15, a shekarar baya.
Duk da samun hauhawan farashin kaya a kasar, Bankin ya samu karin kudaden shigar Bankin, sun karu zuwa kashi 38.9, sabanin kashi 36.1.
Bankin na da yakinin samun ribar shiyar da ta kai ta Naira 4.00, wadda ta kai jimlar ribar shiyar Naira 5.00 da ya samu a shekara.
Shugaba kuma Manajin Darakta na rukunonin Bankin Dakta Adaora Umeoji, da yake yin bayani kan wannan nasarra da Bankin ya samu ya sanar da cewa, nasarar da Bankin ya samu a shekarar, ta nuna irin jajircewar da Bankin ya ke ci gaba da yi, wajen gudanar da ayyukansa, musamman ta hanyar yin amfani da fasahar zamani.
“Zamu kuma ci gaba da mayar da hankali wajen kara habaka fanninin mu na hada-hadar kudade, kara inganta ayyukan mu da farantawa abokan huddar mu da masu ruwa da tsaki rai,”. Inji Bankin Dakta Adaora.
A cewar Shugaban na rukunonin Bankin na Zenith, za mu kuma ci gaba da kara karfafa wanzar da shugabancin mu a fannin hada-hadar kudade na kasar nan.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Naira tiriliyan da Bankin ya
এছাড়াও পড়ুন:
HKI Ta Rufe Filin Saukar Jiragen Sama Na Ben Gorion Tare Da Dauke Jiragenta Zuwa Waje
Mai magana da yawun hukumar da take kula da filin saukar jiragen sama ta Ben Gorion ta sanar a yau Asabar cewa an rufe filin saukar jiragen saman har zuwa wani lokaci a nan gaba, bayan da aka dauke dukkanin jiragen sama zuwa kasashen Cyprus, Greece da kuma Amurka.
Mai Magana da yawun hukumar filin saukar jiragen saman na Ben Gorion Lisa Daiper ta bayyana ce; Babu wani lokaci takamaimai da aka tsayar domin sake bude filin saukar jiragen saman na Ben Gorion.”
A gefe daya jaridar “Maariv’ ta bayyana cewa; An dauke dukkanin jiragen sama zuwa filayen jiragen saman a kasashen turai.
Haka nan kuma ta kara da cewa; An dauki 14 daga cikin jiragen saman na HKI zuwa filin saukar jiragen saman a Laranka da Papus dake tsibirin Cyprus da su ne filayen jiragen sama na nahiyar turai mafi kusa da HKI.
Su kuwa jiragen da shugabannin ‘yan sahayoniya suke shiga an kai su ne zuwa filin jirgin sana na birnin Athenia na kasar Girka, wasu kuwa zuwa kasashen Bulgari da Faransa.
Dauke jiragen na ‘yan sahayoniya dai ya zo ne saboda tsoron kar makamai masu linzami na Iran su isa gare su.