Ma’aikatar harkokin wajen Iran ta sanar da cewa: Za a gudanar da zaman tattaunawa kan Shirin makamashin nukuliyar Iran zagaye na biyu ne a birnin Muscat na kasar Oman

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran Isma’il Baqa’i ya sanar da cewa: Zaman tattaunawa zageye na biyu wanda ba na kai tsaye ba, tsakanin Iran da Amurka zai kasance ne a birnin Muscat fadar mulkin kasar Oman.

Baghaei ya yi watsi da rade-radin da ake yi kan inda za a gudanar da zagaye na biyu na tattaunawar kai tsaye tsakanin Iran da Amurka, Baghaei ya ce, “Bayan tuntubar juna, an yanke shawarar cewa birnin Muscat ne zai karbi bakwancin zagaye na biyu na shawarwarin, wanda za a yi a ranar Asabar mai zuwa.”

Wani abin lura a nan shi ne, an gudanar da shawarwari ba na kai tsaye ba tsakanin Iran da Amurka a ranar Asabar tsakanin ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi da manzon Amurka na musamman kan yankin gabas ta tsakiya Steve Witkoff dangane da batun Shirin makamashin nukiliyar Iran da kuma dage takunkumin da aka kakaba mata na rashin adalci da baya kan tubalin ka’ida. Tattaunawar ta samu halartar mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Isma’il Baqa’i da mataimakin ministan harkokin wajen Iran kan harkokin siyasa Majid Takht-e Ravanchi, da mataimakin ministan harkokin waje kan harkokin shari’a da na kasa da kasa Kazem Gharibabadi, da manyan masu shiga tsakani kan batun dage takunkumi da batun Shirin makamashin nukiliya, da kuma kwararrun da suka dace.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: harkokin wajen Iran

এছাড়াও পড়ুন:

Xi Jinping Ya Bukaci A Hada Karfi Wajen Farfado Da Kasar Sin

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amurka ta sake laftawa wasu kamfaninin mai na Iran takunkumi
  • Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga , Sun Ceto Fasinjoji 6 A Taraba
  • Iran Da Iraki Sun Ce An Kammala Shimfida Layin Dogo Daga Shalamcheh Zuwa Basra
  • Nazarin CGTN: Ana Kara Bayyana Rashin Gamsuwa Da Sabuwar Gwamnatin Amurka Daga Ciki Da Wajen Kasar
  • Babu Wata Tattaunawa Tsakanin Sin Da Amurka Game Da Batun Haraji
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jadadda Cewa: Duk Wani Harin Wuce Gona Da Iri Kan Iran Zai Fuskanci Mayar Da Martani
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Ci Gaba Da Killace Gaza Da Kashe Mutane, Laifi Ne Da Ba A Taba Yin Irinsa Ba
  • Xi Jinping Ya Bukaci A Hada Karfi Wajen Farfado Da Kasar Sin
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Tattauana Da Shugaban Hukumar IAEA
  • Takht Ravanji: Iran Ba Za Ta Taba Yin Tattaunawa Akan Dakatar Da Tace Sanadarin Uranium Ba