Aminiya:
2025-11-02@17:17:54 GMT

’Yan sanda sun gayyaci Sarki Sanusi domin amsa tambayoyi

Published: 5th, April 2025 GMT

Hedikwatar ’yan sandan Nijeriya ta gayyaci Sarkin Kano na 16 Muhammadu Sanusi II domin amsa tambayoyi kan wani lamari da ya faru a lokacin bikin Sallah a Kano.

A baya dai rundunar ’yan sanda tare da sauran wasu jami’an tsaro a jihar sun soke duk wani hawan bikin Sallah, musamman jerin gwanon dawakai a jihar, saboda dalilan tsaro.

Motar fasinja ta kama wuta wasu sun tsallake rijiya da baya Rashin tsaro a Filato ya wuce rikicin manoma da makiyaya – Muftwang

Sai dai a yayin da Sarkin ke tattaki domin halartar Sallah a filin Idi na Ƙofar Mata a ranar 30 ga watan Maris, an caka wa wani ɗan banga da ke kare Sarkin wuƙa har lahira, yayin da wasu da dama suka jikkata.

Bayan faruwar lamarin, wasu sun shaida wa majiyar Daily Nigerian cewa tun da farko babban Sufeton ’yan sandan ƙasar, Kayode Egbetokun ya umarci Kwamishinan ’yan sandan jihar da ya kama sarkin.

Kamar yadda aka samu rahoto, Kwamishinan ya bayyanawa Sufeto Janar ɗin cewa, lamarin ba shi da alaƙa da keta dokar hana hawan Sallah, kuma Sarkin bai yi amfani da dawakai wajen ziyartar gidan gwamnati ba kamar yadda al’adar ta tanada.

Sufeta Janar ya umurci sashen leƙen asiri na rundunar da ta karbe fayil ɗin ƙarar tare da gayyatar Sarkin zuwa Abuja domin amsa tambayoyi.

A wata wasiƙar gayyata da ya sanya wa hannu Kwamishina ’yan sanda CP Olajide Ibitoye, sun gayyaci sarkin da ya gurfana a gaban sashen tattara bayanan sirri na rundunar a ranar Talata 8 ga Afrilu da ƙarfe 10 na safe.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Sarki Sanusi II

এছাড়াও পড়ুন:

PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu ’yan tsagin Wike

Rikici a babbar jam’iyyar adawa ta PDP, na ƙara ƙamari, bayan da jam’iyyar ta dakatar da sakatarenta na ƙasa, Sanata Samuel Anyanwu, da wasu da ake ganin ’yan tsagin Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike ne.

Mai magana da yawun jam’iyyar na ƙasa, Debo Ologunagba ne, ya sanar da dakatarwar bayan wani taro da Kwamitin Ayyuka na Ƙasa (NWC), ya gudanar a hedikwatar jam’iyyar da ke Abuja.

Zargin Kisan Kiristoci: Maganar Trump a kan Najeriya tsagwaron ƙarya ce — Shehu Sani Zaɓen Tanzania: Shugaba Samia ta yi tazarce da kashi 97 an ƙuri’u

Sauran da aka dakatar sun haɗa da Mai Bai wa jam’iyyar Shawara kan Harkokin Shari’a, Kamaldeen Ajibade (SAN); Sakataren Tsara Harkokin Jam’iyya, Umar Bature; da Mataimakin Mai Bai wa jam’iyyar Shawara kan Harkokin Shari’a.

Rahotanni sun bayyana cewa waɗanda aka dakatar ba sa halartar tarukan jam’iyyar.

An dakatar da su na tsawon wata ɗaya, sannan aka miƙa lamarinsu ga Kwamitin Ladabtarwa na jam’iyyar PDP domin gudanar da bincike.

Waɗanda aka dakatar ’yan tsagin Wike ne, kuma sun raba ƙafa a rikicin da jam’iyyar ke fuskanta tun bayan zaɓen 2023.

Idan ba a manta ba, a ranar Juma’a ne, wata Babbar Kotu a Babban Birnin Tarayya, ta dakatar da PDP daga shirin gudanar da babban taronta da aka tsara yi a Ibadan, Jihar Oyo, a ranar 15 da 16 ga watan Nuwamba, 2025.

Sai dai jam’iyyar ta ce za ta ɗaukaka ƙara kan hukuncin, kuma hakan ba zai hana ta ci gaba da shirye-shiryen gudanar da taron ba.

Wasu daga cikin ’ya’yan jam’iyyar sun ce rashin jituwa a PDO shi ne babban dalilin da ya sa aka kai ƙarar taron’ kotu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tsaro: Taimakonmu Amurka ya kamata ta yi maimakon barazana — Kwankwaso
  • Tsaro: Taimakonmu Amurka ya kamata ta yi maimakon ba barazana ba — Kwankwaso
  • Kisan Kiristoci: Ba zan yaƙi ƙasar iyayena kan labaran ƙarya ba — Sojan Amurka
  • PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu ’yan tsagin Wike
  • Gwamna Namadi Ya Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Gwamnatin Jigawa Ta Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4m
  • Yan Nijeriya Na Ɗanɗana Kuɗarsu Kan Jinkirta Cire Tallafin Mai – Sarki Sanusi
  • Matsalar Talauci Da Rashin Tsawon Rai Da ‘Yan Nijeriya Ke Fuskanta
  • Matsalar Tsaro: Ko Sabbin Shugabannin Rundunar Soji Za Su Kawo Sauyi?