A shekarar 2004, lokacin da Olusegun Obasanjo ya ayyana dokar ta-ɓaci a Filato, matakin ya fuskanci suka daga jama’a da ɓangaren shari’a.

Masana doka da ‘yan siyasa sun yi Allah-wadai da matakin da Tinubu ya ɗauka, inda Dokta Reuben Abati ya bayyana shi a matsayin “laifi da za a iya tuhumar Tinubu a kai”.

Ya ce Shugaban Ƙasa ba shi da ikon rushe zaɓaɓɓun shugabanni na jiha.

Bugu da ƙari, Sambauna ya caccaki yadda Gwamnatin Tinubu ke nuna bambanci wajen raba wa matasa tallafi.

Ya ce: “Seyi Tinubu ya bayar da kayan abinci a Arewa a matsayin tallafi, amma a Kudu yana bayar da tallafin kuɗi domin mutane su dogara da kansu wajen bunƙasa kasuwanci. Wannan nuna bambanci ne da bai dace ba.”

Amma, ya buƙaci gwamnati da ta girmama doka da ƙa’idojin dimokuraɗiyya, inda ya ce wannan mataki na Tinubu babbar barazana ce ga mulkin dimokuraɗiyya a Nijeriya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Bashar Sambauna Dokar Ta ɓaci Gwamna Fubara

এছাড়াও পড়ুন:

Bin Hanya Daya Da Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Muhimmin Mataki Ne Na Ba Da Tabbaci Ga Huldar Ciniki Da Tattalin Arzikin Sin Da Amurka

Kafofin yada labarai na kasa da kasa na matukar zura ido kan taron farko na tsarin tattaunawa game da tattalin arziki da cinikayyar Sin da Amurka da aka gudanar tsakanin ranekun 9 zuwa 10 ga watan nan da muke ciki a London na kasar Burtaniya.

An yi muhimmin shawarwarin ne kan matsaya daya bisa manyan tsare-tsaren da shugabannin kasashen biyu suka cimma a ran 5 ga watan nan. A wadannan raneku 2, wakilan Sin da Amurka sun yi mu’ammala mai zurfi cikin sahihanci, kuma sun amince da tabbatar da matsaya daya da shugabannin kasashen biyu suka cimma ta wayar tarho da ba da tabbaci kan ci gaban da aka samu a yayin tattaunawar ciniki da tattalin arziki da aka gudanar a watan Mayun da ya gabata a Geneva.

Ban da wannan kuma, kasashen biyu sun samu sabon ci gaba kan batutuwan ciniki da tattalin arziki da suka tasa a gaba. Kazalika, bangarorin biyu sun nace ga bin hanya iri daya da tabbatar da matsaya daya da suka cimma.

A ganin wani farfesa na kwalejin koyar da ilmin diflomasiyya ta kasar Sin Li Haidong, tsarin tattaunawa da kasashen biyu suka cimma na bayyana niyyarsu ta tabbatar da huldarsu yadda ya kamata, kuma zai daidaita bambancin ra’ayinsu a sabon mataki da ma warware batutuwan ciniki da tattalin arziki da suka tasa a gaba, kana da ingiza bunkasa huldarsu a wannan bangare cikin kwanciyar hankali. A sa’i daya kuma, ci gaban da suka samu na biyan bukatun al’ummun duniya, tare da bayar da ingantaccen karfin raya tattalin arzikin duniya baki daya. (Amina Xu)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • APCn Kaduna Ta Mara Wa Tinubu, Uba Sani Da Kakakin Majalisa Abbas Baya Don Wa’adi Na Biyu
  • An Yi Zanga-zangar Nuna Goyon Baya Ga Kin Amincewa Da Bakin Haure A Amurka 
  • Wakilin Sin: Matakin Amurka Game Da Harajin Kwastam Bai Yi La’akari Da Rarar Cinikayyar Hidimomi Ba
  • Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA
  • Gwamnatin Tarayya Ta Himmatu Wajen Inganta Karfin Sashen Fetur Da Gas Na Cikin Gida
  • Bin Hanya Daya Da Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Muhimmin Mataki Ne Na Ba Da Tabbaci Ga Huldar Ciniki Da Tattalin Arzikin Sin Da Amurka
  • Abin da muke da shi a Najeriya ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba ce — Fayemi
  • Gwamnan Gombe Ya Yi Allah Wadai Da Kisan Da ‘Yan Daba Suka Yi Wa Amadi Kasiran
  • Majalisar Tarayya Na Ƙoƙarin Zama Ƴar Amshin Shata – Saraki
  • Cikin Shekaru 2, Tinubu Ya Karɓo Bashi Fiye da Shugabannin Nijeriya 3 – Obi