Cutar sanƙarau ta kashe sama da mutum 50 a Sakkwato da Kebbi
Published: 14th, March 2025 GMT
Jihohin Sakkwato da Kebbi na fuskantar ƙalubale sakamakon cutar sanƙarau da ta ɓulla a jihohin, inda rahotanni suka tabbatar da cewa cutar ta kashe aƙalla mutum 50, yayin da sama da mutum 200 suka kamu da cutar.
A Jihar Kebbi, ƙananan hukumomin Aliero, Jega, da Gwandu ne suka fi fuskantar matsalar, inda cutar ta fara yaɗuwa kafin a ɗauki matakan gaggawa.
A Jihar Sakkwato kuwa, ƙaramar hukumar Tambuwal ce ta fi fama da cutar, lamarin da ya sa hukumomin lafiya suka sanar da ɗaukar matakan daƙile cutar domin hana ta yaɗuwa zuwa sauran yankunan.
Dalilin Yawaitar CutarMasana kiwon lafiya sun danganta yawaitar cutar da tsananin zafi da ake fama da shi a yankin Arewa Maso Yamma, wanda ke haifar da bushewar iska da kuma saurin bazuwar ƙwayoyin cutar sanƙarau.
Rashin isassun matakan rigakafi da kuma ƙarancin kula da lafiyar jama’a a wasu yankuna na daga cikin dalilan da suka sa cutar ke bazuwa cikin sauri.
Matakan da Aka ƊaukaGwamnatocin jihohin Kebbi da Sakkwato sun ce sun fara ɗaukar matakan gaggawa, inda ake gudanar da allurar rigakafi domin daƙile cutar, musamman ga ƙananan yara da tsofaffi, waɗanda suka fi fuskantar barazanar kamuwa da cutar.
Hakazalika, an ƙara wayar da kan jama’a kan alamomin cutar da matakan kariya, domin daƙile yaɗuwarta a cikin al’umma.
Abubuwan da Jama’a Ke BuƙataDuk da matakan da hukumomi ke ɗauka, har yanzu jama’a na buƙatar ƙarin taimako, musamman wajen samun ingantattun cibiyoyin lafiya da isassun magunguna.
Akwai buƙatar gaggauta aika ƙarin kayayyakin kula da lafiya da ƙarfafa rigakafi domin hana aukuwar cutar a nan gaba.
A halin yanzu, hukumomin lafiya na ci gaba da sa ido kan lamarin, tare da jan hankalin jama’a da su guje wa cunkoso da kuma kai marasa lafiya asibiti da wuri idan suka fara ganin alamomin cutar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: lafiya Sakkwato Sanƙarau
এছাড়াও পড়ুন:
An kashe mafarauta 10 a Adamawa
Aƙalla wasu mutum 10 mafarauta sun rasa rayukansu yayin aikin ceto a ƙauyen Kopire da ke Ƙaramar Hukumar Hong ta Jihar Adamawa.
Shugaban ƙungiyar mafarautan Nijeriya reshen Arewa maso Gabas, Shawulu Yohanna ne ya tabbatar wa Aminiya hakan a ranar Talata.
Wani abin fashewa ya kashe mutum 26 a Borno An dawo da wutar lantarki a Sifaniya da PortugalA cewarsa, ajali ya katse hanzarin mafarautan ne yayin wani arbatu da mayaƙan Boko Haram da suka yi musu kwanton ɓauna a jeji.
Ya bayyana cewa, mafarautan sun tunkari maharan ne bayan samun bayanan sirri da ke nuna cewa suna shirin kai hari.
“Abin takaicin shi yadda ake yi wa Gwamnan Borno ƙafar ungulu a ƙoƙarin da yake yi na ganin an kawo ƙarshen wannan hare-hare a yankin,” in ji shi.
Yohanna ya bayyana damuwa kan yadda mayaƙan Boko Haram ke ci gaba da ƙara ƙarfi a bayan nan da ke zama abin fargaba ga mazauna yankunan da abin ya shafa.
“Mun samu labarin cewa wani jirgi mai saukar ungulu ne yake jigilar mayaƙan daga sansaninsu zuwa wuraren da suke sheƙe ayarsu ba tare fuskantar wata tirjiya ba.
“Amma ina mai tabbatar da cewa muddin Gwamnatin Tarayya ta ɗauki mataki ta hanyar tanadar makamai na zamani, za a kawo ƙarshen waɗannan maƙiya cikin lokacin ƙanƙani.”
Ya roƙi Gwamnatin Tarayya da ta tanadar wa mafarauta da ’yan sa-kai manyan makamai na zamani domin kawo ƙarshen mayaƙan Boko Haram a yankin.
Wannan harin dai na zuwa ne ƙasa da sa’o’i 12 da wasu ’yan ta’adda suka kashe fiye da mutum 30 ciki har da mata da ƙananan yara a ƙananan hukumomin Kala Balge da Gambarou Ngala da ke jihar.