Aminiya:
2025-11-02@16:57:48 GMT

Gobara ta yi ajalin uwa da ’ya’yanta a Ondo

Published: 18th, February 2025 GMT

Ana fargabar cewa gobara ta yi ajalin wata uwa da ’ya’yanta biyu a yankin Onipakala da ke Ƙaramar Hukumar Ondo West a Jihar Ondo.

Bayanai sun ce musibar ta auku ne da tsakar daren Lahadi yayin da jama’a ke sharar barci, lamarin da ya jefa makwabta cikin zullumi.

Saudiyya ta bai wa Kano da Abuja tallafin dabino albarkacin watan Ramadana Mutum biyu sun shiga hannu kan yi wa ’yar shekara 12 fyaɗe a Yobe

Aminiya ta ruwaito cewa, zuwa wayewar gari Litinin, matar da ’ya’yanta —Bukola da Ifeoluwa— sun ƙone ƙurmus a sakamakon gobarar.

Wani maƙwabcinsu da ya buƙaci a sakaya sunansa, ya ce tun tsakar dare gobarar ta tashi amma ana ji ana gani ta rutsa da mutanen uku saboda babu wata hanya da za a iya ceto rayuwarsu.

Shugaban ƙungiyar masu gidajen haya, Mista Adegbulu, ya bayyana takaicin yadda ’yan kwana-kwana suka gaza kawo ɗauki a sanadiyyar rashin ruwan kashe gobara da suka yi iƙirarin ya yanke musu.

“Mun kira su a wayar tarho a lokacin da gobarar ta tashi, amma sai suka shaida mana cewa ruwa da sauran sunadaran kashe gobarar ya yanke musu.

“Kuma nan da nan ma jami’in ya kashe wayarsa,” in ji shi.

Aminiya ta yi ƙoƙarin jin ta bakin ofishin Hukumar Kashe Gobara da ke Akure, amma lamarin ya ci har zuwa lokacin haɗa wannan rahoton.

Mazauna da dama sun bayyana alhini kan aukuwar lamarin da kawo yanzu ba a kai ga gano musabbabinsa ba.

Funmilayo Odunlami-Omisanya, mai magana da yawun rundunar ’yan sandan jihar, ta tabbatar da faruwar lamarin.

Ta bayyana cewa tuni an miƙa gawarwakin mamatan zuwa Babban Asibitin Ondo.

Wannan iftila’i na zuwa ne ƙasa da mako guda da wasu ƙananan yara biyu ’yan gida ɗaya suka riga mu gidan gaskiya a sanadiyyar wata gobara da ta tashi a wani gida a birnin Akure.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: ya ya Gobara jihar Ondo Uwa

এছাড়াও পড়ুন:

Kisan Kiristoci: Za mu kai hari Najeriya — Trump

Shugaban Amurka Donald Trump ya yi barazanar amfani da ƙarfin soji kan Najeriya matuƙar gwamnatin ƙasar ba ta dakatar da kisan da ’yan ta’adda masu iƙirarin jihadi ke yi wa Kiristoci ba.

A yammacin jiya Asabar ne Trump ya umarci Ma’aikatar Yaƙin Amurka ta Pentagon da ta soma tsara yadda za a kai hari Nijeriya bayan da ya yi zargin cewa ana yi wa Kiristoci kisan gilla a ƙasar.

Cikin wani saƙo da ya wallafa  a shafinsa na Truth Social, Trump ya ce Amurka a shirye ta ke ta aike da sojoji da manyan makamai cikin Najeriya don bai wa Kiristocin kariya.

Barazanar shugaban na Amurka na zuwa ne kwana guda bayan ya yi iƙirarin cewa an kashe Kiristoci aƙalla 3,100 a Nijeriya ba tare da ya bayyana takamaimai inda ya samu waɗannan alƙaluma ba.

“Muddin gwamnatin Nijeriya ta ci gaba da bari ana kashe Kiristoci, Amurka za ta dakatar da dukkan tallafin da take bai wa Nijeriya nan-take, kuma mai yiwuwa za ta shiga wannan ƙasƙantacciyar ƙasar, cike da ƙarfin gwiwa domin kawar da ’yan ta’adda masu kaifin kishin Musulunci waɗanda ke yin wannan ta’asa,” in ji Trump.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza
  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • Kisan Kiristoci: Za mu kai hari Najeriya — Trump
  • Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
  • Sanata Sunday Marshall Katung Ya Sauya Sheka Zuwa Jam’iyyar APC
  • Gwamnatin Jihar Kwara Ta Kafa Kwamitoci 2 Don Tantance Wadanda Suka Yi Ritaya
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • ’Yan bindiga sun sace fasinjoji a cikin motocin bas a Kogi
  • Ana zargin ɗa da kashe mahaifinsa a Kano saboda hana shi ƙara aure
  • Borno ta fara fitar da kayan robobi zuwa ƙasashen waje – Zulum