Aminiya:
2025-07-30@23:26:48 GMT

Gobara ta yi ajalin uwa da ’ya’yanta a Ondo

Published: 18th, February 2025 GMT

Ana fargabar cewa gobara ta yi ajalin wata uwa da ’ya’yanta biyu a yankin Onipakala da ke Ƙaramar Hukumar Ondo West a Jihar Ondo.

Bayanai sun ce musibar ta auku ne da tsakar daren Lahadi yayin da jama’a ke sharar barci, lamarin da ya jefa makwabta cikin zullumi.

Saudiyya ta bai wa Kano da Abuja tallafin dabino albarkacin watan Ramadana Mutum biyu sun shiga hannu kan yi wa ’yar shekara 12 fyaɗe a Yobe

Aminiya ta ruwaito cewa, zuwa wayewar gari Litinin, matar da ’ya’yanta —Bukola da Ifeoluwa— sun ƙone ƙurmus a sakamakon gobarar.

Wani maƙwabcinsu da ya buƙaci a sakaya sunansa, ya ce tun tsakar dare gobarar ta tashi amma ana ji ana gani ta rutsa da mutanen uku saboda babu wata hanya da za a iya ceto rayuwarsu.

Shugaban ƙungiyar masu gidajen haya, Mista Adegbulu, ya bayyana takaicin yadda ’yan kwana-kwana suka gaza kawo ɗauki a sanadiyyar rashin ruwan kashe gobara da suka yi iƙirarin ya yanke musu.

“Mun kira su a wayar tarho a lokacin da gobarar ta tashi, amma sai suka shaida mana cewa ruwa da sauran sunadaran kashe gobarar ya yanke musu.

“Kuma nan da nan ma jami’in ya kashe wayarsa,” in ji shi.

Aminiya ta yi ƙoƙarin jin ta bakin ofishin Hukumar Kashe Gobara da ke Akure, amma lamarin ya ci har zuwa lokacin haɗa wannan rahoton.

Mazauna da dama sun bayyana alhini kan aukuwar lamarin da kawo yanzu ba a kai ga gano musabbabinsa ba.

Funmilayo Odunlami-Omisanya, mai magana da yawun rundunar ’yan sandan jihar, ta tabbatar da faruwar lamarin.

Ta bayyana cewa tuni an miƙa gawarwakin mamatan zuwa Babban Asibitin Ondo.

Wannan iftila’i na zuwa ne ƙasa da mako guda da wasu ƙananan yara biyu ’yan gida ɗaya suka riga mu gidan gaskiya a sanadiyyar wata gobara da ta tashi a wani gida a birnin Akure.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: ya ya Gobara jihar Ondo Uwa

এছাড়াও পড়ুন:

Araqchi: Tattaunawar Nukiliya Wani Zabi Ne Mai Muhaimmanci Wanda Ya Karfafa Matsayin Iran A Duniya

Ministan harkokin wajen kasar Iran ya bayyana cewa: Tattaunawar makamashin nukiliya wani zaɓi ne mai mahimmanci wanda ya ƙarfafa matsayin Iran a duniya

Ministan harkokin wajen kasar Iran Seyyed Abbas Araqchi ya tabbatar da cewa; Kasarsa ta shiga shawarwarin makamashin nukiliya ba na                         kai tsaye ba da Amurka bisa wata cikakkiyar shawarar kasa. Ya kara da cewa; Wannan mataki na diflomasiyya ya karfafa kimar Iran a duniya, bayan da ta samu goyon bayan kasashe fiye da 120 wadanda suka yi Allah wadai da cin zarafin da yahudawan sahayoniyya suka yi wa Iran a baya-bayan nan.

Hakan dai ya zo ne a yayin wata ganawa da aka yi da Araghchi, inda ya yi nazari kan batutuwan da suka shafi makamashin nukiliyar Iran da ma matakan da aka dauka na yin shawarwari da kasashen yammacin duniya. Ya yi bayanin cewa, manufar yarjejeniyar makamashin nukiliyar ta ginu ce bisa ka’ida mai ma’ana, ta yadda Iran za ta dauki matakai na karfafa kwarin gwiwa domin dage takunkumin kanta.

Jami’in na Iran ya yi nuni da cewa, a lokacin da gwamnatin Trump ta Amurka ta bayyana burinta na yin shawarwari kan batun makamashin nukiliyar, Iran ta bayyana shirinta na shiga tattaunawa bisa wannan manufa, tare da jaddada cewa, ba za ta amince da duk wani sharadi da zai kawo cikas ga shirinta na nukiliya ko kuma dakatar da ayyukan inganta sinadarin Uranium ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu ya karɓi baƙuncin Abdulmumin Jibrin Kofa
  • Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya
  • Tinubu ya naɗa sabon shugaban hukumar kashe gobara ta ƙasa
  • Ambaliya ta yi ajalin mutum 30 a China
  • Kwale-kwale Ya Kife Da Fasinjoji 16 A Karamar Hukumar Taura
  • Wani mutum ya mutu yayin raba faɗar ma’aurata 
  • Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa
  • Mutanen Sweida Na Kasar Siriya Suna Fama da Rashin Abinci da Ruwa
  • An kashe ’yan ta’adda 45 a Neja
  • Araqchi: Tattaunawar Nukiliya Wani Zabi Ne Mai Muhaimmanci Wanda Ya Karfafa Matsayin Iran A Duniya