Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Muhimmancin Gudanar Da Safarar Teku
Published: 16th, February 2025 GMT
Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana cewa; Tsaron ruwa bai kamata ya zama kayan aikin matsin lamba kan kasashen waje ba
Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya jaddada cewa: Bai kamata tsaron teku ya zama wani makami na matsin lamba kan kasashen waje ba, sai dai ya zama sakamakon hadin gwiwa tsakanin kasashen yankin.
A cikin jawabin da ya gabatar a wajen bude taron ministocin kasashen tekun Indiya karo na 8 a birnin Muscat na kasar Oman a yau Lahadi, Araqchi ya ce: A yau mun hadu a kasar da aka sani tsawon shekaru aru-aru a matsayin gada da ta hada tsakanin gabas da yamma, kuma tsakanin manyan wayewa da al’ummomi na kusa da na nesa.
Ya kara da cewa: Kasar Oman, mai masaukin bakin al’adu, ba kawai ta kasance a tsawon lokaci tana taka rawa ba ce a fannin tattalin arziki, har ma ta kasance wata alama ce ta taimakekkeniya da tattaunawa da diflomasiyya mai ma’ana a yankin tekun Indiya, wanda a ko da yaushe ke kan gaba wajen ci gaban duniya, mai taka muhimmiyar rawa a makomar tattalin arzikin kasa da kasa.
Ministan harkokin wajen ya kara da cewa: A tsawon tarihi, tekuna sun kasance tamkar kofofin da suke hada tsakanin wayewa, ba iyakokin kasa ba tsawon dubban shekaru, tekun Indiya ba ruwa ne kawai, har ma ya kasance babbar hanyar kasuwanci, musayar al’adu da ci gaban wayewa. Wannan hanya ta hada ‘yan kasuwa daga gabar tekun Indiya zuwa Afirka, daga tsibiran Indonesiya zuwa Tekun Fasha, da kuma daga Iran zuwa Tekun Bahar Maliya. A lokacin da hanyoyin kasa suke da tsawo kuma ba su da aminci, teku ce ta hada kasashe masu tasowa da kuma samar da sabbin damammaki.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: tekun Indiya
এছাড়াও পড়ুন:
Araghchi: “Ba ma wasa game da batun inganta uranium, wanda hakkin al’ummar Iran ne”
Ministan harkokin wajen Iran Seyed Abbas Araghchi ya tabbatar da cewa Iran ba za ta amince da duk wata tattaunawa kan dakatar da shirinta na inganta makamashin Uranium gaba daya ba.
Ya bayyana hakan ne a gefen ziyarar da shugaban kasar ya kai kasar Oman, inda ya jaddada cewa, bai kamata tattaunawa da Amurka za ta hada da batun ba wanda Tehran ba za a amince da shi ba.
Araghchi ya ce, ana ci gaba da tattaunawa da Amurka, amma batun tace uranium shi ne ya kasance babban abin da ake samun sabani.
Ya kuma kara da cewa, an yi shawarwari da ministan harkokin wajen Oman game da shirya wani sabon zagaye na shawarwari tsakanin Iran da Amurka.
Ministan ya jaddada cewa Iran na daukar tace sinadarin Uranium a matsayin wani hakki na kasa wanda ba za’a iya tauye mata ba, kamar yadda yarjejeniyar hana yaduwar makaman nukiliya ta tanada.