An kama gungun masu yi wa Boko Haram da ’yan bindiga safarar babura
Published: 28th, January 2025 GMT
Rundunar ’yan sandan Nijeriya ta samu nasarar cafke gungun wasu masu yi wa mayaƙan Boko Haram da ’yan bindiga safarar babura a jihohin Neja da Kaduna.
Galibai dai ’yan ta’adda a Arewacin Nijeriya sukan yi amfani da babura wajen gudanar da harkokin sufuri domin sheƙe ayarsu ta garkuwa da satar mutane da kai wa al’ummomi hare-hare.
Da yake zantawa da manema labarai a hedikwatar ’yan sanda da ke Abuja a ranar Talatar nan, mai magana da yawun rundunar, Benneth Igweh, ya ce sun samu nasarar ce ta hanyar bayanan sirri, inda suka cafke wasu mutum uku a Ƙaramar Hukumar Suleja ta Jihar Neja.
Igweh ya bayyana sunayen ababen zargin da ke hannu da suka haɗa da Shamsudden Yunusa mai shekara 30 da Zahraddeen Saidu mai shekara 25 sai kuma Mustapha Haruna mai shekara 22.
Ya bayyana cewa sun samu jimillar babura 22 a hannun ababen zargin da kuma tarin mukullai da wayoyin hannu.
Ya yi ƙarin haske da cewa ababen zargin sun ƙware wajen sauya fasalin babura da aka sato suna bayar da haya ko sayar wa miyagu ciki har da mayaƙan Boko Haram da suka yi sansani a jihohin Neja da Kaduna.
Ya ƙara da cewa, jagora a cikin ababen zargin—Shamsudden—ya bayyana cewa ya kan sayar da duk babur ɗaya kan farashin Naira dubu 200 zuwa 250.
“Ya faɗa mana cewa a kwanan nan ya karɓi kafin alƙalami har Naira dubu 250 a hannun wani mai suna Ibrahim Kabiru da ke zaune a Ƙaramar Hukumar Birnin Gwari domin kawo masa babura ƙirar Bajaj.
“Shi kuma Zahraddeen shi ne mai jigilar kai babu ga masu saye, inda ya shaida mana cewa ko a kwanan nan ya kai wasu babura da ya karɓo a hannun wani mai suna Mustapha a garin Suleja.
“Shi kuma Mustapha ya ƙware wajen sauya fasalin babura da yi musu gyare-gyare gabanin a sayar wa abokan hulɗarsu,” in ji Igweh.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Babura Boko Haram Jihar Kaduna Jihar Neja ababen zargin
এছাড়াও পড়ুন:
Ƴansanda Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 2, Sun Ceto Mutane 11 A Delta Da Katsina
Rundunar Ƴansandan Nijeriya, tare da haɗin gwuiwar sauran hukumomin tsaro, ta samu nasarar cafke mutane biyu da ake zargi da garkuwa da mutane tare da ceto mutane 11 da aka sace a jihohin Delta da Katsina. Wannan na cikin ƙoƙarin ci gaba da yaƙi da miyagun laifuka a faɗin ƙasa.
A jihar Katsina, an daƙile wani yunƙurin garkuwa da mutane a ranar 8 ga Yuni, 2025, a hanyar Danmusa zuwa Mara Dangeza, inda jami’an haɗin gwuiwa suka yi artabu da ‘yan bindiga. Bayan musayar wuta mai tsanani, jami’an suka tilasta masu laifin guduwa da raunukan harbi tare da kuɓutar da mutum 11 da suka sace ba tare da raunuka ba.
Yanzu-yanzu: Gwamnan Delta Oborevwori Ya Fice Daga PDP Zuwa APC Kocin Kano Pillars Usman Abdullahi Ya Ajiye AikinsaA jihar Delta, jami’an CP-Special Assignment sun cafke wani Abubakar Hassan, wanda ake zargin jagoran gungun masu garkuwa da mutane ne da ke aiki a jihohi da dama. Bayan gudanar da bincike, ya jagoranci jami’ai zuwa maboyarsu a dajin Ozoro, inda aka ƙwato bindigogi AK-47 guda biyu da harsasai. Hakanan, wani direba, Obi Ezekiel, ya shiga hannu yayin da aka gano bindiga ƙirar gida da alburusai a motarsa.
Babban Sufeton Ƴansanda na ƙasa, IGP Kayode Egbetokun, ya yaba da ƙwarewa da kwazon jami’an tsaro a waɗannan ayyuka, tare da jan hankali cewa rundunar zata ci gaba da gudanar da irin wadannan farmaki don tabbatar da cewa babu mafaka ga masu aikata laifi a duk faɗin Nijeriya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp