An kama gungun masu yi wa Boko Haram da ’yan bindiga safarar babura
Published: 28th, January 2025 GMT
Rundunar ’yan sandan Nijeriya ta samu nasarar cafke gungun wasu masu yi wa mayaƙan Boko Haram da ’yan bindiga safarar babura a jihohin Neja da Kaduna.
Galibai dai ’yan ta’adda a Arewacin Nijeriya sukan yi amfani da babura wajen gudanar da harkokin sufuri domin sheƙe ayarsu ta garkuwa da satar mutane da kai wa al’ummomi hare-hare.
Da yake zantawa da manema labarai a hedikwatar ’yan sanda da ke Abuja a ranar Talatar nan, mai magana da yawun rundunar, Benneth Igweh, ya ce sun samu nasarar ce ta hanyar bayanan sirri, inda suka cafke wasu mutum uku a Ƙaramar Hukumar Suleja ta Jihar Neja.
Igweh ya bayyana sunayen ababen zargin da ke hannu da suka haɗa da Shamsudden Yunusa mai shekara 30 da Zahraddeen Saidu mai shekara 25 sai kuma Mustapha Haruna mai shekara 22.
Ya bayyana cewa sun samu jimillar babura 22 a hannun ababen zargin da kuma tarin mukullai da wayoyin hannu.
Ya yi ƙarin haske da cewa ababen zargin sun ƙware wajen sauya fasalin babura da aka sato suna bayar da haya ko sayar wa miyagu ciki har da mayaƙan Boko Haram da suka yi sansani a jihohin Neja da Kaduna.
Ya ƙara da cewa, jagora a cikin ababen zargin—Shamsudden—ya bayyana cewa ya kan sayar da duk babur ɗaya kan farashin Naira dubu 200 zuwa 250.
“Ya faɗa mana cewa a kwanan nan ya karɓi kafin alƙalami har Naira dubu 250 a hannun wani mai suna Ibrahim Kabiru da ke zaune a Ƙaramar Hukumar Birnin Gwari domin kawo masa babura ƙirar Bajaj.
“Shi kuma Zahraddeen shi ne mai jigilar kai babu ga masu saye, inda ya shaida mana cewa ko a kwanan nan ya kai wasu babura da ya karɓo a hannun wani mai suna Mustapha a garin Suleja.
“Shi kuma Mustapha ya ƙware wajen sauya fasalin babura da yi musu gyare-gyare gabanin a sayar wa abokan hulɗarsu,” in ji Igweh.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Babura Boko Haram Jihar Kaduna Jihar Neja ababen zargin
এছাড়াও পড়ুন:
Ana zargin mace da kashe ’yar uwarta a kan N800 din barkono
Rundunar ’Yan Sanda ta Jihar Ondo ta tabbatar da kama wata mata mai suna Iluyemi Bosede bisa zargin kashe yayarta, Tewogboye Omowumi, a Akure, babban birnin jihar.
A cewar sanarwar da Jami’in Hulɗa da Jama’a na rundunar, Olayinka Ayanlade, ya fitar a ranar Talata, ya ce lamarin ya faru ne a ranar shida ga Satumba, 2025, bayan wata sa’insa da ta kaure tsakanin matar da marigayiyar kan Naira 800.
Tun Tinubu yana Gwamna ba abin da ya fi shahara da shi kamar tara haraji – Adebayo DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Doya A Wasu Kasuwannin NajeriyaJami’in ya bayyana cewa Bosede ta ture ’yar uwarta har ta faɗi ƙasa, lamarin da ya haifar da mutuwarta.
Ya ce, “Binciken farko ya nuna cewa Iluyemi Bosede ta je wurin yayar tata, Tewogboye Omowumi mai shekaru 35, domin karbar bashinta na N800 na kudin tumatir da barkono. Sai dai tankiyar da ta fara a matsayin ƙaramin sabani ta rikide zuwa tashin hankali, inda ake zargin Bosede ta riƙe kayan marigayiyar har ta faɗi ƙasa.”
“Abin takaici, duk da an garzaya da marigayiyar asibiti don samun kulawar gaggawa, likitoci sun tabbatar da mutuwarta tun kafin a fara ba ta taimako. Wannan lamari ya nuna yadda ƙaramin sabani zai iya rikidewa zuwa mummunar husuma idan ba a magance shi cikin lumana ba.”
Bayan faruwar lamarin, rundunar ta ce ta kama wadda ake zargi kuma tana tsare da ita a halin yanzu, yayin da bincike ke ci gaba.
Rundunar ta kuma tabbatar da cewa za a gurfanar da wadda ake zargin a gaban kotu bayan kammala bincike, domin ta girbi abin da ta shuka.