Aminiya:
2025-11-02@19:37:55 GMT

Gwamna ya aike wa majalisa dokar haramta auren jinsi ɗaya a Kano

Published: 12th, September 2025 GMT

Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya amince da mika kudirin dokar haramta auren jinsi daya, luwadi da madugo ga Majalisar Dokokin Jihar domin amincewa da shi a matsayin doka.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar ranar Juma’a, ya ce gwamnan ya bayar da umarnin ne yayin zaman majalisar zartarwar jihar karo na 31 da aka gudanar a reshen gidan gwamnati da ke Kwankwasiyya City a Kano.

Likitoci sun tsunduma yajin aiki a fadin Najeriya Ambaliyar ruwa ta tsayar da ababen hawa cak a tsakiyar birnin Abuja

Gwamna Yusuf ya ce gwamnatinsa ba za ta sassauta kan koyarwar addinin Musulunci ba, yana mai jaddada cewa dole ne Kano ta ci gaba da kare al’adu da addinin mutanen jihar.

Ya ce kudirin dokar ya haramta auren jinsi da kuma wasu dabi’u na madugo da luwadi, wadanda gwamnati ke dauka a matsayin haramtattu.

“Babu wani yanayi da za mu amince da ayyukan da suka sabawa addininmu da al’adunmu su samu gindin zama a Kano. Wannan gwamnati na da alhakin kare mutuncin zamantakewarmu,” in ji gwamnan.

Da zarar majalisar dokoki ta amince da kudirin ya zama doka, duk wanda aka samu da laifin aikata ko tallata auren jinsi da makamancin haka zai fuskanci hukunci mai tsauri.

Gwamna Yusuf ya nuna kwarin gwiwarsa cewa ‘yan majalisar za su amince da kudirin cikin gaggawa, la’akari da muhimmancinsa ga tarbiyya da zamantakewar mutanen jihar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Luwadi

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yansanda Sun Ceto Mutum Ɗaya, Sun Kama Mace Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Dajin Kwara 

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai October 30, 2025 Manyan Labarai Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda  October 30, 2025 Manyan Labarai Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC October 30, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su
  • Zargin Kisan Kiristoci: Maganar Trump a kan Najeriya tsagwaron ƙarya ce — Shehu Sani
  • Gwamna Uba Sani Ya Bayyana Tsare-tsaren Ci Gaban Kaduna a Taron Duniya a Dubai.
  • Gwamna Namadi Ya Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Sharrin son auren Mai Wushirya aka yi min — Mansura Isa
  • An yi garkuwa da Mataimakin Shugaban Majalisar Dokokin Kebbi
  • Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 
  • Shugabannin Kudancin Kaduna za su karrama Janar  Christopher Musa 
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Daliban Makarantar Kudi Suka Fi Na Gwamnati Kokari
  • ‘Yansanda Sun Ceto Mutum Ɗaya, Sun Kama Mace Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Dajin Kwara