Tinubu ya bayar da umarnin a sake karya farashin kayan abinci
Published: 11th, September 2025 GMT
Shugaban Kasa Bola Tinubu ya umarci Kwamitin Majalisar Zartarsa ta Kasa da ya dada aiwatar da matakan da za su kara karya farashin kayan abinci a fadin Najeriya.
Karamin Ministan Noma da Samar da Abinci, Sanata Aliyu Sabi Abdullahi ne ya bayyana hakan ranar Laraba a Abuja.
EFCC ta tsare Mele Kyari kan binciken matatun mai Macron ya karɓi baƙuncin Tinubu a Fadar ElyseeYa ce umarnin ya shafi tabbatar da cewa an rage farashin sufurin kayan amfanin gona ba tare da kashe makudan kudade ba.
“Shugaban Kasa ya bayar da umarni ga Kwamitin Majalisar Zartarsa ta Kasa wanda dama yanzu haka yana nan yana kokarin ganin an saukaka hanyoyin sufurin amfanin gona a fadin kasar nan, da su dada karya farashin kasa da yadda yake yanzu haka a kasuwa,” in ji ministan, kamar yadda ya fada yayin wani taron kara wa juna sani da aka shirya wa ’yan jaridar Fadar Shugaban Kasa.
Najeriya, wacce ita ce kasa mafi yawan jama’a a nahiyar Afirka dai na fama da matsalar abinci, wacce ta ta’azzara tun bayan cire tallafin man fetur da tsadar sufuri da kuma matsalolin tsaro a kan manyan hanyoyi da ya kawo cikas ga jigilar kayan amfanin gona.
Duk da matakan da gwamnati ta ce tana dauka dai, har yanzu miliyoyin ’yan Najeriya ba sa iya samun wadataccen abinci.
Sai dai ministan ya ce umarnin na Tinubu wani bangare ne na burin shi na tabbatar da samar da isasshe kuma lafiyayyen abinci da kowa zai iya saye a Najeriya.
Ministan ya kuma ce nan ba da jimawa ba gwamnati za ta fito da wani sabon shiri na bunkasa kasar noma da zai bunkasa amfanin da ake samu sannan ya samar wa da manoma rance domin tallafa wa manoman da ke yankunan karkara.
Ko a watan Yunin da ya gabata, sai da Shugaba Tinubu ya jaddada cewa Najeriya na kan hanyar tsayawa da kafarta a harkar samar da abinci, la’akari da manufofin da gwamnatinsa ta bullo da su.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Karya farashi Kayan abinci
এছাড়াও পড়ুন:
Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu
A yau Litinin ne tawagogin kasashen Sin da Amurka, suka sake tattaunawa a rana ta biyu, game da batutuwan tattalin arziki da cinikayya a birnin Madrid na kasar Sifaniya. A jiya Lahadi, sassan biyu sun gudanar da zaman farko ne a fadar Santa Cruz, inda ofishin ministan harkokin wajen kasar ta Sifaniya yake.
A cewar kakakin ma’aikatar cinikayyar kasar Sin, sassan biyu za su tattauna batutuwan da suka hada da matakin Amurka na kakaba jerin haraji daga bangare guda, da keta matakan kayyade fitar da hajoji, da batun dandalin TikTok. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp