Macron ya karɓi baƙuncin Tinubu a Fadar Elysee
Published: 11th, September 2025 GMT
Shugaban Faransa, Emmanuel Macron ya karɓi baƙuncin Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu a Fadar Elysee da ke birnin Paris.
Wannan dai wani ɓangare ne na hutun aiki da Tinubun yake yi a ƙasashen Turai da ya tafi a makon jiya.
INEC ta amince da jam’iyyar haɗaka ta ADC Yadda zanga-zangar adawa da rashawa ta rikiɗe zuwa tarzoma a NepalHakan na ƙunshe cikin wani saƙo da mai magana da yawun shugaban ƙasar, Bayo Onanuga ya wallafa tare da hotunan ganawar a ranar Laraba.
A cewar sanarwar, “Shugaba Macron ya karɓi baƙuncin Shugaba Tinubu domin cin abincin rana a fadar Elysee da ke birnin Paris.”
Tinubu ya fara hutun kwanaki 10 daga cikin hutun shekara da ya dauka wanda ya soma tun daga makon da ya gabata, inda ya bar Nijeriya a ranar Alhamis.
Fadar shugaban ƙasar ta bayyana cewa zai yi hutun ne a ƙasashen Birtaniya da Faransa.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Peter Obi ya kai wa Obasanjo ziyara
Ɗan takarar jam’iyyar Labour a zaɓen shugaban ƙasa na 2023, Peter Obi, ya ziyarci tsohon shugaban ƙasa, Olusegun Obasanjo, da kuma sabon Olubadan na Ibadan, Rashidi Ladoja, a wani zagayen ganawa da manyan ’yan siyasa gabanin zaɓen 2027.
Obi, wanda ke ƙoƙarin ƙara yauƙaƙa zumunci da manyan shugabanni a fadin ƙasar, ya bayyana cewa ziyarar na da alaƙa da burinsa na ganin an samu shugabanci na gaskiya da riƙon amana a Najeriya.
An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar KEDCO ya ƙaryata asibitin AKTH kan mutuwar majinyata saboda ɗauke wutaA wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X, Obi ya bayyana cewa ziyararsa ta musamman zuwa Ibadan na da nufin girmama Rashidi Ladoja, wanda aka naɗa a matsayin Olubadan, da kuma jaddada muhimmancin Ibadan a siyasa, zamantakewa, da tattalin arzikin ƙasar.
“Na kai ziyara don girmama sabon Olubadan, Rashidi Ladoja, wanda ƙwarewarsa a matsayin tsohon sanata, gwamna, kuma attajiri za ta taimaka wajen ɗaga martabar Ibadan,” in ji Obi.
Ya ƙara da cewa tattaunawarsa da Obasanjo da Ladoja na da nasaba da ci gaban Najeriya da kuma shugabanci da ke da burin sauya al’umma ta fuskar gaskiya da adalci.
Ziyarar Obi na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da shirye-shiryen siyasa gabanin babban zaɓen shekarar 2027, inda ake hasashen zai sake tsayawa takarar shugaban ƙasa.