DSS ta warware tankiyar da ke tsakanin NUPENG da Dangote
Published: 10th, September 2025 GMT
Hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) ta samu nasarar warware tankiyar da ke tsakanin Matatar Dangote da Ƙungiyar Ma’aikatan Dakon Man Fetur da Gas ta Najeriya (NUPENG).
Wannan na zuwa ne bayan wani zama da aka gudanar a babban ofishin DSS da ke Abuja, inda rahotanni ke cewa shugabannin NUPENG sun umurci mambobinsu da su dakatar da yajin aikin da aka fara a faɗin ƙasar.
Aminiya ta ruwaito cewa, Ministan Kuɗi, Wale Edun; Ministan Kwadago da Ayyuka, Mohammed Maigari Dingyadi; da Ƙaramin Ministan Ƙwadago, Nkeiruka Onyejeocha, duk sun halarci zaman.
Haka zalika, tawagar Kamfanin Dangote ƙarƙashin jagorancin Alhaji Sayyu Dantata ta halarci taron.
Daga cikin shugabannin ƙwadago da suka halarta akwai Mista Akpouha Williams na NUPENG, Mitsa Benson Upah na Ƙungiyar Ƙwadago ta Najeriya (NLC), da Dokta NA Toro na TUC.
A jiya Litinin ce aka tashi baram-baram a wajen taron tattunawar sulhu da aka yi tsakanin ƙunyiyoyin ƙwadago na NLC da TUC da kuma wakilan kamfanin Dangote.
Kungiyar NUPENG ce ta fusata a sakamakon matakin da Matatar Dangote ta dauka na fara jigilar mai zuwa gidajen mai da ke faɗin ƙasar.
NUPENG ta ce muddin matatar mai ta Dangote ta fara jigilar mai zuwa gidajen man da ke jihohi, to dubban ma’aikatan da ke aiki a daffo-daffo da kuma direbobin da ke tuƙa manyan motoci sama da dubu 30, za su rasa aikinsu.
Ita ma ƙungiyar masu gidajen mai da iskar gas NOGASA, ta nuna goyon bayanta a kan matakin da NUPENG din ta ce za ta ɗauka na shiga yajin aiki.
To sai dai kuma ƙungiyar masu gidajen mai da iskar gas ta Arewacin Najeriya wato AROGMA ta ce tana maraba da matakin da Matatar Ɗangote ta ɗauka na yin dakon mai zuwa gidajen man a faɗin ƙasar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Matatar Dangote
এছাড়াও পড়ুন:
Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare
A ranar 30 ga wata ne shugabannin kasashen Sin da Amurka suka gana da juna a birnin Busan na kasar Koriya ta Kudu, lamarin da ya jawo hankulan kasa da kasa, inda shugabannin 2 suka yi musayar ra’ayoyi dangane da huldar da ke tsakanin kasashen 2 da al’amuran da suka jawo hankulansu. Sun amince da inganta hadin gwiwar kasashen 2 a fannonin tattalin arziki da cinikayya da makamashi da kyautata mu’amalar al’adu.
A yayin ganawar, shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya jaddada cewa, yana son hada kai da shugaba Donald Trump na Amurka wajen aza harsashi mai kyau na raya huldar da ke tsakanin kasashen 2, tare da samar wa juna kyakkyawan yanayin samun ci gaba. A nasa bangaren, shugaba Trump ya ce, kasar Sin, abokiyar Amurka ce mafi girma. Kasashen 2 za su hada kansu wajen samun nasarar gudanar da manyan ayyuka da dama a duniya. Nan gaba Amurka da Sin za su kara samun nasara a hadin gwiwarsu. Shugabannin 2 sun amince su rika yin mu’amala da juna. Shugaba Trump yana sa ran kai ziyara a kasar Sin a farkon shekara mai zuwa, ya kuma gayyaci shugaba Xi ya ziyarci Amurka.
Masharhanta sun yi nuni da cewa, ganawar shugabannin 2 ta sanya tagomashi kan kyautatuwar huldar da ke tsakanin Sin da Amurka, ta kuma tsara manufar raya huldar kasashen 2 a nan gaba, tare da kwantar da hankulan kasashen duniya.
Abubuwan tarihi da kuma hakikanin abubuwa sun nuna cewa, wajibi ne Sin da Amurka su zama abokan juna. A wannan muhimmin lokaci, ganawar da shugabannin kasashen 2 suka yi ta sake tsara manufar kyautata da raya huldar da ke tsakanin kasashen 2. Muddin kasashen 2 suka aiwatar da muhimman daidaito da shugabannin 2 suka cimma, da mutunta ruhin adalci, tare da martaba juna da samun moriyar juna, to, za a raya huldar da ke tsakanin kasashen 2 ba tare da wata matsala ba, da kuma kara samar da kwanciyar hankali da tabbaci a duniya. (Tasallah Yuan)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA