DSS ta warware tankiyar da ke tsakanin NUPENG da Dangote
Published: 10th, September 2025 GMT
Hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) ta samu nasarar warware tankiyar da ke tsakanin Matatar Dangote da Ƙungiyar Ma’aikatan Dakon Man Fetur da Gas ta Najeriya (NUPENG).
Wannan na zuwa ne bayan wani zama da aka gudanar a babban ofishin DSS da ke Abuja, inda rahotanni ke cewa shugabannin NUPENG sun umurci mambobinsu da su dakatar da yajin aikin da aka fara a faɗin ƙasar.
Aminiya ta ruwaito cewa, Ministan Kuɗi, Wale Edun; Ministan Kwadago da Ayyuka, Mohammed Maigari Dingyadi; da Ƙaramin Ministan Ƙwadago, Nkeiruka Onyejeocha, duk sun halarci zaman.
Haka zalika, tawagar Kamfanin Dangote ƙarƙashin jagorancin Alhaji Sayyu Dantata ta halarci taron.
Daga cikin shugabannin ƙwadago da suka halarta akwai Mista Akpouha Williams na NUPENG, Mitsa Benson Upah na Ƙungiyar Ƙwadago ta Najeriya (NLC), da Dokta NA Toro na TUC.
A jiya Litinin ce aka tashi baram-baram a wajen taron tattunawar sulhu da aka yi tsakanin ƙunyiyoyin ƙwadago na NLC da TUC da kuma wakilan kamfanin Dangote.
Kungiyar NUPENG ce ta fusata a sakamakon matakin da Matatar Dangote ta dauka na fara jigilar mai zuwa gidajen mai da ke faɗin ƙasar.
NUPENG ta ce muddin matatar mai ta Dangote ta fara jigilar mai zuwa gidajen man da ke jihohi, to dubban ma’aikatan da ke aiki a daffo-daffo da kuma direbobin da ke tuƙa manyan motoci sama da dubu 30, za su rasa aikinsu.
Ita ma ƙungiyar masu gidajen mai da iskar gas NOGASA, ta nuna goyon bayanta a kan matakin da NUPENG din ta ce za ta ɗauka na shiga yajin aiki.
To sai dai kuma ƙungiyar masu gidajen mai da iskar gas ta Arewacin Najeriya wato AROGMA ta ce tana maraba da matakin da Matatar Ɗangote ta ɗauka na yin dakon mai zuwa gidajen man a faɗin ƙasar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Matatar Dangote
এছাড়াও পড়ুন:
Fira Ministan Spain: Bai Kamata A Rika Barin “Isr’ila” Tana Shiga Gasar
Wasannin Duniya Ba
Fira ministan kasar ta Spain ya bayyana hakan ne dai a yayin da yake nuna jin dadinsa danagen da gagarumar Muzaharar da mutanen kasar su ka yi ta nuna kin amincewarsu da shigar kasar ta Yahudawa cikin tseren kekune.
Fira ministan kasar ta Spain Pedro Sánchez Pérez ya ce: ” Har zuwa lokacin da za a kawo karshen kisan kiyashi a Gaza, bai kamata a kyale Isra’ila ta rika shiga cikin gasar wasannin kasa da kas aba.
A yau litinin ne dai Fira ministan kasar ta Spain ya gabatar da jawabi gabanin taron ‘yan majalisa masu wakiltar jam’iyyun gurguzu, ya yi ishara da taho mu gamar da aka yi a tsakanin masu kin jinin kisan kiyashin da HKI take yi wa Falasdinawa da masu goyon bayanta, sannan ya kara da cewa; a kodayaushe ba mu aminta da tashin hankali ba.
Mutane 20 ne dai su ka jikkata a yayin wannan taho mu gama din a babban birnin kasar ta Spain,Madrid.
Fira ministan Pedro Sánchez Pérez ya kuma yi wa hukumomin wasanni na duniya tamabya da cewa; Me ya sa aka haramtawa Rasha shiga cikin wasannin kasa da kasa saboda yakin Ukiraniya,amma ba a kori Isra’ila ba?.
Al’ummar kasar Spain da mahukuntanta suna cikin nag aba-gaba a cikin nahiyar turai wajen nuna kin amincewa da yi wa mutanen Gaza kisan kiyashi.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Shugaban Kasar Iran Ya Gana Da Sarkin Kasar Qatar A Birnin Doha September 15, 2025 Dan Kasar Iran Mai Kirkira Ya Sami Kyautar Yabo A Kasar China September 15, 2025 Fizishkiyan: Wajibi Ne Musulmi Su Hada Kai Domin Dakatar Da Laifukan HKI September 15, 2025 Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Qatar, Turkiyya, Pakistan Da Labanon A Doha September 15, 2025 Kwamitin Kolin Tsron Kasar Iran Ya Amince Da Yarjejeniyar Da Aka Cimma Da Hukumar IAEA September 15, 2025 Jami’in Kasar Yemen Ya Aike Da Sako Ga Mahalarta Taron Birnin Doha Na Kasar Qatar September 15, 2025 Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada Sakamakon Kisan Kiyashin ‘Yan Sahayoniyya A Gaza Ya Kusaci 65,000 September 15, 2025 Gwamnatin Sudan Ta Ce: Babu Sulhu Da ‘Yan Tawayen Kasar Na Kungiyar Rapid Support Forces September 15, 2025 Kasashen Larabawa da na Musulmi na taron gaggawa kan harin Isra’ila a Qatar September 15, 2025 Hamas ta bukaci kasashen musulmi da na Larabawa su dauki mataki mai tsari kan Isra’ila September 15, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci