Aminiya:
2025-09-17@23:15:02 GMT

TUC ta yi barazanar shiga yajin aiki kan ƙara harajin man fetur

Published: 9th, September 2025 GMT

Ƙungiyar ƙwadago a Najeriya TUC ta yi barazanar shiga yajin aiki dangane da matakin da Gwamnatin Tarayya ta ce za ta ɗauka na ƙara harajin kaso 5 cikin 100 a farashin duk litar man fetur.

A yayin da ƙungiyar ta yi watsi da matakin, ta kuma kwatanta aiwatar da hakan a matsayin ganganci da mugunta ga tattalin arzikin ƙasar.

Dalilin da muka yi watsi da buƙatar dawowar Sanata Natasha — Majalisar Dattawa NAJERIYA A YAU: Tasirin Takaddamar NUPENG Da Dangote A Kan Tattalin Arzikin Najeriya

A bayan nan ne dai Gwamnatin Tarayyar ta sanar da ɗaukar wannan mataki da zai fara aiki a farkon watan Janairun 2026, domin samun kuɗaɗen shiga da za a yi amfani da su wajen gina hanyoyi da sauran manyan ayyuka a ƙasar.

Sai dai tuni ƙungiyar ta TUC ta bai wa gwamnatin wa’adin kwanaki 14 da ta janye wannan matakin, ko kuma ta ɗauki matakin da take ganin ya dace.

A cewar, ƙungiyar ƙwadagon, cikin matakin da za ta ɗauka har da rufe manyan sassan gwamnati musamman masu samar da kuɗaɗen shiga.

Wata sanarwa da Festus Osifo da kuma Nuhu Toro, shugabannin ƙungiyar suka sanyawa hannu, sun ce a halin da ake ciki ’yan Najeriya na cikin ƙangin biyan haraje-haraje barkatai.

Shugabannin ƙungiyar ƙwadagon, sun ce sabon harajin ba abu ne da zai yiwu ba, don haka ya zama wajibi gwamnati ta dakatar da shi.

A cewarsu, har yanzu ’yan Najeriya ba su gama farfaɗowa daga ƙangin da cire tallafin man fetur ya jefa su ba, baya ga lalacewar darajar Naira.

Kazalika, ƙungiyar ta ce ta fara sanar da sassanta na jihohi don shirin tafiya yajin aiki, idan hakan ta kama.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gwamnatin tarayya Haraji Litar Man Fetur Yajin aiki

এছাড়াও পড়ুন:

Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

Duk da cewar an yi yarjejeniya tsakanin ɓangarorin biyu, rikici ya sake ɓarkewa bayan NUPENG ta ce Dangote bai cika alƙawari ba.

Amma matatar ta musanta zargin, inda ta bayyana cewa ma’aikatanta na da damar shiga ƙungiya idan sun so, amma ba dole ba ne.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • UNICEF Ya Ba Da Tallafin Kayayyakin Aiki Ga Cibiyoyin Lafiya A Kirikasamma
  • Kwara ETF Ya Dauki Nauyin Karatun Fitattun Dalibai A Matakin Sakandare
  • An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Ta Kama Bisa Kuskuren Safarar Ƙwayoyi
  • Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?
  • ’Yan ‘Mafiya’ na ƙoƙarin kashe matatar man fetur da na gina —Ɗangote
  • NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba
  • Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa