Aminiya:
2025-09-17@21:52:18 GMT

Matatar Dangote ta musanta dakatar da aiki

Published: 8th, September 2025 GMT

Matatar mai ta Dangote ta ƙaryata rahoton da ke cewa za ta iya dakatar da ayyukanta na sarrafa ɗanyen mai har nan da tsawon watanni biyu zuwa uku.

Hakan na ƙunshe cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rukunin kamfanin na Dangote, Anthony Chiejina ya fitar, inda ya bayyana rahoton a matsayin “tsantsar ƙarya” wadda ba ta da tushe balle makama.

Sojoji sun kashe kasurgumin dan ta’adda da yaransa 5 a Kogi

An fara samun masu zawarcin kujerar Firaministan Japan

A wani rahoto da kamfanin dillancin labarai na Reuters ya fitar, ya bayyana cewa, ‘‘akwai yiwuwar rufe sashen matatar man kamfanin wadda ke samar da ganga 650,000 duk rana tsawon watanni biyu zuwa uku saboda aiwatar da wasu gyare-gyare, yana mai ambato shawarar da masana’antar IIR Energy da ke sa ido kan makamashi ta bayar.

A cewar rahoton, tun daga ranar 29 ga watan Agusta aka yi ikirarin rufe sashen matatar man bayan da aka samu matsala ta kwararar mai daga ɓangaren tace man masana’antar.

Kazalika rahoton ya ƙara da cewa, matatar za ta yi ƙoƙarin sake soma aikin tace mai na ganga 204,000 duk rana daga 20 ga watan Satumba, sai dai manyan gyare-gyare da kuma sauya wasu kayan aiki ka iya sanyawa a rufe ta tsawon wasu watanni.

Da yake mayar da martani kan rahoton, Anthony Chiejina, ya bayyana ikirarin a matsayin “labarin ƙarya” yana mai ɗiga ayar tambaya kan dalilin da Reuters zai yi amfani da kalmar ‘yiwuwa’ a rahoton idan har yana da tabbaci kan shirin rufewar matatar, kamar yadda ya shaida wa jaridar Punch a ranar Lahadi.

Kamfanin dillancin labaran Reuters dai ya bayar da rahoton cewa ana sa ran rufe sashen kamfanin Dangote na RFCCU na aƙalla makonni biyu.

Matatar mai ta Dangote, wadda ta soma sarrafa ɗanyen mai a watan Janairun 2024, ta sauƙaƙa harkokin mai na cikin gida, lamarin da kuma ya kawo cikas ga harkar cinikayyar fitar da man fetur daga ƙasashen Turai zuwa Yamma.

Kazalika, kasuwancin fitar da man fetur daga ƙasashen Turai da Birtaniya zuwa Nijeriya ya ragu daga ganga kusan 200,000 a shekarar 2024 zuwa kusan 120,000 a watanni shidan farko na wannan shekara ta 2025, a cewar kafar tattara bayanai ta Kpler.

Haka kuma, matatar ta yi jigilar hanyoyin man fetur guda biyu zuwa gabar tekun Gabas ta Amurka, waɗanda ake sa ran isarsu yankin New York nan gaba a cikin wannan wata.

Wannan dai wani gagarumin ci gaba ne, inda masu sa ido kan masana’antu ke bibiyar lokacin da matatar za ta samar da mai da zai yi gogayya da na Amurka.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Matatar Dangote

এছাড়াও পড়ুন:

KEDCO ya ƙaryata asibitin AKTH kan mutuwar majinyata saboda ɗauke wuta

Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Shiyyar Kano (KEDCO) ya ƙaryata zargin da Asibitin Koyarwa na Aminu Kano (AKTH) ya yi masa, dangane da mutuwar wasu marasa lafiya sakamakon katse wutar lantarki da aka ce kamfanin ya yi.

Asibitin na AKTH ya bayyana damuwarsa a ranar Lahadi kan abin da ya kira abin takaici yana mai cewa mutanen da suka mutu za su iya tsira da ransu da ba a ɗauke wutar ba.

Amma a martanin da ya bayar, Shugaban Sashen Hulɗa da Jama’a na KEDCO, Sani Bala Sani, ya ce asibitin na ƙoƙarin ɓata sunan kamfanin ne kawai, domin an dawo da wutar tun kafin asibitin ya fitar da wannan sanarwar.

Sani ya bayyana cewa matsalar ta samo asali ne daga wani yunƙurin da ake yi na raba ginin asibitin da cibiyoyin lafiya daga gidajen ma’aikatan asibitin.

“Cibiyar asibitin da cibiyoyin lafiya suna da alaƙa da layin 33kV na Zariya Road wanda aka fi ba fifiko wajen raba wuta, kuma suna samun kimanin sa’o’i 22 na wutar lantarki a kullum ƙarƙashin tsarin Band A.

“Amma, shugabannin AKTH sun dage cewa sai gidajen ma’aikata sun ci gaba da kasancewa a layin wutar lantarki ɗaya da cibiyoyin lafiya. Wannan ya janyo barazana ga inganci da kwanciyar hankali na wutar da aka ware wa asibitin.

“An yi ƙoƙari sau da dama don raba gidajen ma’aikata daga cibiyoyin lafiya, amma haƙarmu ba ta kai ga cimma ruwa ba saboda ƙin amincewar shugabannin asibitin. Abin takaici, wannan ya haifar da matsala mai tsanani da ta janyo katsewar wutar da muke ƙoƙarin kaucewa,” in ji KEDCO.

Don tabbatar da wutar lantarki ba tare da katsewa ba ga asibitin, kamfanin KEDCO ya ce yana ci gaba da aikin raba layukan wutar lantarkin biyu. Ya ce annan mataki ya zama dole don tabbatar da inganci, tsaro da kyautata lantarki ga asibitin.

Kamfanin ya kuma zargi asibitin da rashin biyan kuɗin wutar lantarki da gidajen ma’aikata ke amfani da ita, wanda ke shafar ingancin ayyukan samar da wuta na kamfanin.

KEDCO ya ce a cikin wata wasiƙa da ya aike ranar 12 ga Agusta, 2025, Babban Jami’in Kasuwanci na kamfanin, Muhammad Aminu Ɗantata, ya sanar da Shugaban Asibitin AKTH game da shirin dakatar da samar da wutar lantarki ga gidajen ma’aikata da wuraren da ba su da muhimmanci, sakamakon rashin cikakken biyan kuɗin wutar wata-wata.

Wasiƙar ta bayyana cewa:

“Duk da roƙon da aka yi sau da dama, asibitin ya ƙi biyan cikakken kuɗin wutar da yake sha a duk wata.

Wannan ya haifar da bashin wutar lantarki da ya kai ₦949,880,922.45 a watan Agustan 2025.

“An bukaci asibitin ya biya kuɗin watan Agusta 2025 na ₦108,957,582.29 gaba ɗaya cikin kwanakin aiki 10, don kaucewa yanke wuta a wuraren da abin ya shafa,” in ji wasiƙar.

Kamfanin ya ƙuduri aniyar ci gaba da samar da wutar lantarki ba tare da katsewa ba ga AKTH a matsayin babbar cibiyar lafiya.

A ƙarshe, KEDCO ya roƙi shugabannin asibitin da su ba da haɗin kai a aikin raba layukan wutar, wanda ya ce yana da amfani ga marasa lafiya, ma’aikata, da al’umma baki ɗaya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 
  • Microsoft ya ƙwace shafukan wasu kamfanoni 340 a Najeriya
  • NECO ta saki sakamakon jarabawar 2025
  • Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire
  • Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?
  • ’Yan ‘Mafiya’ na ƙoƙarin kashe matatar man fetur da na gina —Ɗangote
  • Taron Doha: Daga matakin Allawadai zuwa matakan kalubalantar laifukan Isra’ila
  • Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar
  • KEDCO ya ƙaryata asibitin AKTH kan mutuwar majinyata saboda ɗauke wuta