Aminiya:
2025-09-17@21:52:06 GMT

Firaministan Japan Shigeru Ishiba ya yi murabus

Published: 7th, September 2025 GMT

Firaministan Japan, Shigeru Ishiba, ya sanar da murabus dinsa a matsayin shugaban jam’iyyar Liberal Democratic Party (LDP), watanni kaɗan bayan jam’iyyarsa ta sha mummunan kaye a zaɓen watan Yuli.

Ishiba ya sanar da matakin ne a ranar Lahadi, duk da cewa a baya ya yi ƙoƙarin kaucewa matsin lambar ‘yan jam’iyyarsa da ke neman ya sauka sakamakon rashin nasarar zaɓen, inda ya dage cewa yana son tabbatar da yarjejeniyar haraji da ƙasar ta ƙulla da Amurka ta fara aiki yadda ya kamata.

’Yan bindiga sun kashe jami’an Sibil Difens 8 a Edo ’Yan ta’adda sun kashe mutum 63 a Borno

“Tun da Japan ta sanya hannu kan wannan yarjejeniya, kuma shugaban Amurka ya rattaba hannu a matsayin doka, mun tsallake babban ƙalubale,” in ji shi.

“Lokaci ya yi da zan miƙa wa sabon jini tutar shugabanci,” ya ƙara da cewa.

Duk da murabus ɗinsa daga shugabancin jam’iyyar, Ishiba zai ci gaba da zama Firaminista har zuwa lokacin da za a gudanar da zaɓen cikin gida domin zaɓen sabon shugaban LDP.

Gidan Talabijin na Al-Jazeera ya ruwaito cewa wannan mataki ya ƙara jefa Japan, wacce ita ce ƙasa ta huɗu mafi girman tattalin arziƙi a duniya, cikin ruɗanin siyasa.

Tun bayan hawansa mulki a watan Oktoba da ya gabata, ɗan siyasar mai shekara 68 ya gamu da manyan ƙalubalai da suka yi sanadin kawar da rinjayen ’yan jam’iyyarsa a majalisun biyu na ƙasar.

Rashin nasarar, wanda aka danganta shi da ƙorafin jama’a kan tsadar rayuwa, ya sa gwamnatin Ishiba ta kasa aiwatar da manufofinta yadda ta tsara.

Yayin da ƙasar ke ƙara faɗawa cikin ruɗanin siyasa, manyan ‘yan jam’iyyarsa musamman daga bangaren ’yan ra’ayin mazan jiya sun matsa masa lambar yin murabus, waɗanda suka ɗora masa alhakin rashin nasara a zaɓen majalisar dattawa na Yuli.

Rahotanni sun ce Ministan Aikin Noma na Japan tare da tsohon Firaministan sun gana da shi a daren ranar Asabar domin shawartarsa da ya yi murabus.

A taron manema labarai da ya kira ranar Lahadi, Ishiba ya tabbatar da murabus ɗinsa, tare da bayyana cewa ya fara shirye-shiryen neman wanda zai gaje shi.

Yayin da ƙasar ke ƙara nutsewa cikin rudanin siyasa, manyan ‘yan jam’iyyarsa musamman daga bangaren ’yan ra’ayin mazan jiya sun matsa masa lamba da ya sauka, suna zarginsa da alhakin sakamakon zaben majalisar dattawa na Yuli.

Rahotanni sun ce Ministan Aikin Noma na Japan tare da tsohon Firayim Minista sun gana da shi a ranar Asabar da dare don shawarce shi ya sauka.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan jam iyyarsa

এছাড়াও পড়ুন:

NDLEA ta kama ɗan Indiya da ƙwaya ta Naira biliyan 3 a Legas

Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta Najeriya (NDLEA) ta kama wani ɗan ƙasar Indiya tare da wasu mutane uku bisa zargin shigo da ƙwayoyin Tramadol da aka ƙiyasta darajarsu ta kai naira biliyan uku (N3bn) zuwa cikin ƙasar.

A cewar NDLEA, wannan shi ne kamen ƙwayoyi mafi girma da hukumar ta yi a cikin shekarar nan, lamarin da ke nuna yadda safarar miyagun ƙwayoyi ke ƙaruwa a ƙasar.

Peter Obi ya kai wa Obasanjo ziyara An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar

Cikin wata sanarwa da hukumar ta fitar, ta bayyana cewa jami’anta sun kama mutanen ne a filin jirgin sama na Murtala Muhammad da ke Legas, bayan sun samu bayanan sirri da suka taimaka wajen gano su.

NDLEA ta bayyana cewa ƙwayoyin Tramadol ɗin da aka gano an shigo da su ne cikin kwalaye a matsayin maganin multivitamins, yayin da ake ƙoƙarin fitar da su daga filin jirgin a wasu manyan motoci.

“Ƙwayoyin da aka kama ba su da wata alaƙa da amfani na lafiya, waɗanda aka shigo da su a ɓoye a matsayin maganin rage kasala da ƙara kuzari (multivitamins),” in ji sanarwar NDLEA.

Rahotanni sun nuna cewa a da likitoci na bayar da Tramadol ne don rage zafi da raɗaɗin ciwo, amma yanzu ta zamo annoba musamman a tsakanin matasa, wadda ke haddasa mummunan maye da illa ga lafiya.

Hukumar ta nuna damuwa game da yadda yawan masu amfani da Tramadol ke ƙaruwa ba wai a Najeriya kaɗai ba, har ma a wasu ƙasashen Afirka, duk da illolin da ƙwayar ke haddasawa, kamar matsalolin taɓin hankali ko ma rasa rai gaba ɗaya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Saudiyya ta saki ’yan Najeriya 3 da ta kama kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi
  • Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
  • ’Yan ‘Mafiya’ na ƙoƙarin kashe matatar man fetur da na gina —Ɗangote
  • ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu
  • NDLEA ta kama ɗan Indiya da ƙwaya ta Naira biliyan 3 a Legas
  • ’Yan sanda sun sasanta rikicin asibitin AKTH da KEDCO
  • Peter Obi ya kai wa Obasanjo ziyara
  • Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato
  • Dole sai mun tantance wa’azi kafin a yi —Gwamnan Neja
  • Sarki Sanusi II ya koka kan yawan cin bashin Najeriya