Tsagin NNPP na ƙasa ya yi watsi da korar Abdulmumin Jibrin Kofa
Published: 7th, September 2025 GMT
Tsagin Jam’iyyar New Nigeria People’s Party (NNPP) ya ƙi amincewa da korar ɗan Majalisar Tarayya mai wakiltar mazaɓar Kiru/Bebeji a Jihar Kano, Abdulmumin Jibrin Kofa.
Hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da Sakataren Jam’iyyar na Ƙasa, Oginni Sunday ya raba wa ’yan jarida ranar Asabar.
Musulman Kudancin Kaduna sun zargi manyan yankin da juya gaskiya Bikin naɗin Sarkin Ibadan yan hana Musulmi Sallar Juma’a — MURICOginni ya yi Allah wadai da korar ɗan majalisar, yana mai cewa babu wata hujja kuma ba su ba da izini ko wani iko na ɗaukar wannan hukunci ba.
Sunday ya ce tuni an sallami shugaban jam’iyyar na Kano, Hashim Dungurawa tare da rukunin tsagin Kwankwasiyya daga jam’iyyarsu ta NNPP.
A bayan nan ne Hashim Dungurawa ya bayyana cewa sun kori ɗan majalisar mai wakiltar mazaɓar Kiru da Bebeji saboda dalilai na cin amana da kuma tallan wani ɗan takara.
“Mun same shi da cin amanar jam’iyya a matakai daban-daban,” in ji Dungurawa.
“Na farko, mun same shi da tallata ɗantakarar shugaban ƙasa na wata jam’iya da ba namu ba.
“Na biyu, ya ce zai iya fita daga jam’iyyar. Wannan ba ƙaramin cin amana ba ne. Na uku, ba ya biyan kuɗin haraji na jam’iyya, duk da cewa akwai doka cewa duk wata akwai abin da zai bayar domin ci gaban jam’iyyar.
“Na huɗu, ba ya zuwa mazaɓarsa. ‘Yan mazaɓarsa kan yi kusan wata biyar ba su ji ɗuriyarsa ba.”
Na amince da hukuncin —KofaA martanin da mayar, Abdulmumi Jibrin Kofa ya sanar da ya amincewa da matakin korarsa da jam’iyyar ta yi.
Sai dai ya bayyana mamakin wannan hukuncin da jamiyyar ta yanke. “Ina da maganganun da na yi ba su yi nauyin da za su ja min kora ba, amma duk da haka ina nan a kan batuna, babu abin da na janye” in shi.
Ya ce ba a gayyace shi ba domin ya kare kansa kan abin da ake zarginsa da aikatawa, “ko a gidan soja, ana ba wanda ake zargi dama ya kare kansa.
“Game da batun rashin biyan kuɗina, ina roƙon jam’iyya ta turo min da lissafin kuɗin nan, zan biya nan take. Babu buƙatar hayaniya ko cin mutunci.”
Ya ce ya so a ce ya ci gaba da zama a jam’iyyar, “amma tun da jam’iyyar ta kore ni, dole in amince da matakin da ta ɗauka.”
Dan majalisar ya ce nan gaba kaɗan zai sanar da matakin da zai ɗauka a game da makomarsa a siyasa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jihar Kano a jam iyyar
এছাড়াও পড়ুন:
Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini ba — Tinubu
Shugaba Bola Tinubu ya mayar wa da Shugaban Amurka, Donald Trump martani cewa Najeriya ba ta yadda da duk wani nau’in zarafin addini.
Tinubu, ya yi wannan bayani ne bayan Trump ya sake sanya Najeriya cikin jerin ƙasashen da ake kiran “Ƙasashen da ke da Babbar Matsala wajen ’Yancin Addini.”
PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu ’yan tsagin Wike Sharrin son auren Mai Wushirya aka yi min — Mansura IsaTrump ya yi iƙirarin cewa Kiristoci a Najeriya na fuskantar barazana, amma ya sha alwashin cewa Amurka za ta kare su.
A cikin wani saƙo da ya wallafa a kafafen sada zumunta, Trump ya rubuta cewa: “Addinin Kirista yana fuskantar babbar barazana a Najeriya. Ana kashe dubban Kiristoci.”
A ranar Asabar, Tinubu ya mayar da martani ta kafar sada zumunta, inda ya ce Najeriya ƙasa ce mai dimokuraɗiyya wadda kundinta ya tabbatar da ’yancin yin addini.
“Najeriya tana da cikakken tanadi a kundinta da ya tabbatar da ’yancin yin addini,” in ji Tinubu.
“Tun daga shekarar 2023, gwamnatina na aiki tare da shugabannin Kiristoci da Musulmai don magance matsalolin tsaro da ke shafar jama’a daga kowane ɓangare da addini.”
Ya ƙara da cewa, kiran Najeriya ƙasa mai matsala wajen gudanar addini ba gaskiya ba ne.
“Za mu ci gaba da kare ’yancin kowane ɗan ƙasa na yin addininsa cikin walwala. Najeriya ba ta goyon bayan zaluncin addini ko kaɗan,” in ji Tinubu.
Ya kuma ce Najeriya za ta ci gaba da haɗa kai da Amurka da sauran ƙasashe domin inganta zaman lafiya da fahimtar juna tsakanin mabiya addinai daban-daban.