NNPP: A tura min lissafin kuɗin da ake bi na zan biya — Kofa
Published: 7th, September 2025 GMT
Ɗan Majalisar Tarayya mai wakiltar Kiru/Bebeji, Abdulmumin Jibrin, ya bayyana mamakinsa game da korarsa daga jam’iyyar NNPP.
Shugaban jam’iyyar na Jihar Kano, Hashimu Dungurawa, ne ya bayyana korar Kofa kan zargin yi wa jam’iyyar zagon ƙasa da kuma rashin biyan kuɗaɗen da ake bin sa.
Boko Haram sun kashe gomman mutane da sojoji a ƙauyen Borno NNPP ta kori Kofa daga jam’iyyar, ta yi barazanar maka shi a kotuYa kuma yi barazanar kai shi kotu idan bai biya kuɗaɗen da ake bin sa ba.
A martaninsa, Kofa, ya ce: “Korata daga NNPP ta zo da mamaki sosai. Ban yi tsammanin tattaunawar da na yi a kafafen yaɗa labarai za ta jawo irin wannan hukunci ba.
“Babu wata gayyata da aka yi min domin na kare kaina, abin da ya saɓa ƙa’ida saboda ba a bai wa mutum dama kare kansa ba.”
Ya ƙara da cewa a shirye yake ya biya bashin kuɗin jam’iyyar ke bin sa ba tare da an je kotu ba.
“Game da batun rashin biyan kuɗina, ina roƙon jam’iyya ta turo min da lissafin kuɗin nan, zan biya nan take. Babu buƙatar hayaniya ko cin mutunci.”
Kofa, ya gode wa NNPP bisa goyon bayan da ya samu a lokacin da yake cikin jam’iyyar, sannan ya gayyaci magoya bayansa da su biyo shi yayin da yake shirin fara sabuwar tafiya a siyasa.
A baya-bayan dai rikicin cikin gida na ci gaba da mamayar NNPP a Jihar Kano, lamarin da ya sanya Sanata mai wakiltar Kano ta Arewa, Kawu Sumaila ya fice daga jam’iyyar tare da komawa APC.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Barazana Kora Siyasa zargi
এছাড়াও পড়ুন:
An kama mabaraci da kuɗaɗen ƙasar waje a Ilorin
Hukumar jin daɗin jama’a ta Jihar Kwara tare da haɗin gwiwar Hukumar Gyaran Hali ta Najeriya sun kama wasu mabarata a titunan Ilorin, ciki har da wasu da aka samu da kuɗaɗen ƙasashen waje.
Daga cikin waɗanda aka kama akwai wani mabaraci mai suna Musa Mahmud daga Jihar Kano, wanda aka samu da takardar daloli.
Musa Mahmud ya shaida wa manema labarai cewa wani ne ya ba shi takardar Dala a Abuja.
Jami’ai sun bayyana damuwa kan yadda masu bara ke riƙe da kuɗaɗen da ba su dace da yanayin rayuwarsu ba.
Mutuwar majinyata: Asibitin Aminu Kano na roƙon KEDCO ya dawo da wutar lantarki Cire tallafin man fetur shi ne abin da ya dace —Sarki Sanusi II“Za mu bincika asalin waɗannan kuɗaɗen da kuma dalilin da ya sa suke da su,” in ji Adebayo Okunola, shugaban cibiyar gyaran hali a Jihar Kwara.
Jami’an gwamnati sun kwashe kusan mutane 40 daga wuraren da suka haɗa da Tipper Garage, Offa Garage, Tank da Geri Alimi Roundabout.
Jami’an sun ce bakwai daga cikin waɗanda aka kama an taɓa kama su a baya, amma sun koma tituna bayan an sako su.
Kwamishinar jin daɗin jama’a ta jihar, Dakta Mariam Imam, ta ce adadin masu bara da aka kama ya ragu sosai idan aka kwatanta da na baya, inda ta ce suna sauya dabaru don su guje wa kama.
Ta roƙi jama’a da su daina ba wa masu bara kuɗi kai tsaye, su maida gudummawarsu ta hanyar wuraren ibada da gidajen marayu.
Jami’an gyaran hali sun ce za a tilasta wa waɗanda aka kama su yi aikin tsaftace tituna a matsayin horo da kuma darasi.
Wasu daga cikin masu barar sun roƙi gwamnati da ta tausaya musu, ba su da wata hanyar rayuwa sai bara.