Aminiya:
2025-11-02@15:25:04 GMT

NNPP: A tura min lissafin kuɗin da ake bi na zan biya — Kofa

Published: 7th, September 2025 GMT

Ɗan Majalisar Tarayya mai wakiltar Kiru/Bebeji, Abdulmumin Jibrin, ya bayyana mamakinsa game da korarsa daga jam’iyyar NNPP.

Shugaban jam’iyyar na Jihar Kano, Hashimu Dungurawa, ne ya bayyana korar Kofa kan zargin yi wa jam’iyyar zagon ƙasa da kuma rashin biyan kuɗaɗen da ake bin sa.

Boko Haram sun kashe gomman mutane da sojoji a ƙauyen Borno NNPP ta kori Kofa daga jam’iyyar, ta yi barazanar maka shi a kotu

Ya kuma yi barazanar kai shi kotu idan bai biya kuɗaɗen da ake bin sa ba.

A martaninsa, Kofa, ya ce: “Korata daga NNPP ta zo da mamaki sosai. Ban yi tsammanin tattaunawar da na yi a kafafen yaɗa labarai za ta jawo irin wannan hukunci ba.

“Babu wata gayyata da aka yi min domin na kare kaina, abin da ya saɓa ƙa’ida saboda ba a bai wa mutum dama kare kansa ba.”

Ya ƙara da cewa a shirye yake ya biya bashin kuɗin jam’iyyar ke bin sa ba tare da an je kotu ba.

“Game da batun rashin biyan kuɗina, ina roƙon jam’iyya ta turo min da lissafin kuɗin nan, zan biya nan take. Babu buƙatar hayaniya ko cin mutunci.”

Kofa, ya gode wa NNPP bisa goyon bayan da ya samu a lokacin da yake cikin jam’iyyar, sannan ya gayyaci magoya bayansa da su biyo shi yayin da yake shirin fara sabuwar tafiya a siyasa.

A baya-bayan dai rikicin cikin gida na ci gaba da mamayar NNPP a Jihar Kano, lamarin da ya sanya Sanata mai wakiltar Kano ta Arewa, Kawu Sumaila ya fice daga jam’iyyar tare da komawa APC.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Barazana Kora Siyasa zargi

এছাড়াও পড়ুন:

PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu da ke da alaƙa da Wike

Rikici a babbar jam’iyyar adawa ta PDP, na ƙara ƙamari, bayan da jam’iyyar ta dakatar da sakatarenta na ƙasa, Sanata Samuel Anyanwu, da wasu da ake ganin ’yan tsagin Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike ne.

Mai magana da yawun jam’iyyar na ƙasa, Debo Ologunagba ne, ya sanar da dakatarwar bayan wani taro da Kwamitin Ayyuka na Ƙasa (NWC), ya gudanar a hedikwatar jam’iyyar da ke Abuja.

Zargin Kisan Kiristoci: Maganar Trump a kan Najeriya tsagwaron ƙarya ce — Shehu Sani Zaɓen Tanzania: Shugaba Samia ta yi tazarce da kashi 97 an ƙuri’u

Sauran da aka dakatar sun haɗa da Mai Bai wa jam’iyyar Shawara kan Harkokin Shari’a, Kamaldeen Ajibade (SAN); Sakataren Tsara Harkokin Jam’iyya, Umar Bature; da Mataimakin Mai Bai wa jam’iyyar Shawara kan Harkokin Shari’a.

Rahotanni sun bayyana cewa waɗanda aka dakatar ba sa halartar tarukan jam’iyyar.

An dakatar da su na tsawon wata ɗaya, sannan aka miƙa lamarinsu ga Kwamitin Ladabtarwa na jam’iyyar PDP domin gudanar da bincike.

Waɗanda aka dakatar ’yan tsagin Wike ne, kuma sun raba ƙafa a rikicin da jam’iyyar ke fuskanta tun bayan zaɓen 2023.

Idan ba a manta ba, a ranar Juma’a ne, wata Babbar Kotu a Babban Birnin Tarayya, ta dakatar da PDP daga shirin gudanar da babban taronta da aka tsara yi a Ibadan, Jihar Oyo, a ranar 15 da 16 ga watan Nuwamba, 2025.

Sai dai jam’iyyar ta ce za ta ɗaukaka ƙara kan hukuncin, kuma hakan ba zai hana ta ci gaba da shirye-shiryen gudanar da taron ba.

Wasu daga cikin ’ya’yan jam’iyyar sun ce rashin jituwa a PDO shi ne babban dalilin da ya sa aka kai ƙarar taron’ kotu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya
  • PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu ’yan tsagin Wike
  • PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu da ke da alaƙa da Wike
  • Kotu ta dakatar da gudanar da babban taron PDP
  • Kotu ta dakatar da babban taron PDP na ƙasa
  • Kotu ta dakatar da babban taron PDP
  • Kotu ta tsige dan majalisar da ya sauya sheka zuwa APC
  • Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP
  • An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo
  • Gwamnatin Gombe ta saurari ra’ayoyin jama’a kan kasafin kuɗin 2026