Aminiya:
2025-09-17@21:49:44 GMT

NNPP ta kori Kofa daga jam’iyyar, ta yi barazanar maka shi a kotu

Published: 6th, September 2025 GMT

Jam’iyyar NNPP ta Jihar Kano, ta kori Abdulmumin Jibrin Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar mazaɓar Kiru/Bebeji.

Jam’iyyar ta zarge shi da yi mata zagon ƙasa da kuma gaza biyan kuɗaɗen da ake binsa.

’Yan bindiga sun kashe jami’an NSCDC 8, sun sace ɗan China a Edo APC ta yi barazanar hukunta “Yaran Badaru” a Jigawa

Shugaban NNPP na jihar, Hashim Sulaiman Dungurawa ne, ya bayyana haka ranar Asabar a Kano.

Ya ce Jibrin ya daɗe yana fitowa a kafafen watsa labarai yana zagin jam’iyya da shugabanninta.

Wannan na zuwa ne kwana ɗaya bayan da Kofa, ya ce zai iya barin NNPP, inda ya ce yana da ƙwarewar da zai iya yanke shawara kan makomar siyasarsa.

Dungurawa, ya ce Kofa ba shi da ƙarfin da zsi iya lashe zaɓe a ƙashin kansa ba don darakar Kwankwasiyya da NNPP ba.

Ya ce a baya Kofa ya kasa samun nasara lokacin da ya yi takara a jam’iyyar APC.

Shugaban ya ƙara da cewa an kafa kwamitin sulhu domin yin sulhu da shi bayan hirar da ya yi a gidan talabijin na Channels.

A cewarsa daga baya Kofa ya ci gaba da fitowa a kafafen yaɗa labarai yana biyayya ga wasu da ba ’yan jam’iyyar ba.

“Saboda haka mun kore shi. Ba shi da wani abin da zai ƙara wa jam’iyya,” in ji Dungurawa.

Haka kuma, ya zargi Kofa da ƙin biyan kuɗin da jam’iyya ta wajabta, inda ya ce za su kai shi kotu domin karɓo haƙƙinsu.

Kan jita-jitar Kofa na iya komawa APC, Dungurawa, ya ce hakan ba zai rage wa NNPP ƙarfi ba.

Ya jaddada cewa siyasa tana tafiya da ƙungiyoyi, kuma Kwankwasiyya na nan daram ƙarƙashin jagorancin Rabiu Musa Kwankwaso.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: hira Kora Kwankwasiyya Siyasa zargi

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Ambaliyar ruwa na cigaba da salwantar da dukiyoyi da rayukan al’ummomi da dama a sassa daban-daban na Najeriya.

 

Ko a farkon makon nan, hukumomi sun yi gargadin cewa akwai yiwuwar samun ambaliyar a jihohi akalla 11.

Sai dai wasu alummomin tuni suka dauki matakai don rage barnar da ambaliyar ka iya yi musu.

NAJERIYA A YAU: Masu Nau’in Jinin AS Sun Fi Masu Nau’in AA Lafiya DAGA LARABA: Dalilan Da Suka Sa Nayi Yunkurin Kashe Kaina Har Sau Uku

A kan wadannan matakai shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu bai shirya gudanar da sahihin zaɓe ba a 2027 – Buba Galadima
  • Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu
  • Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi
  • Tun Tinubu yana Gwamna ba abin da ya fi shahara da shi kamar tara haraji – Adebayo
  • DSS ta maka Sowore da Facebook a Kotu kan cin zarafin Tinubu
  • DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu
  • Taron Doha: Daga matakin Allawadai zuwa matakan kalubalantar laifukan Isra’ila
  • Dole sai mun tantance wa’azi kafin a yi —Gwamnan Neja
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa
  • Mutuwar majinyata: Asibitin Aminu Kano na roƙon KEDCO ya dawo da wutar lantarki