Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC
Published: 6th, September 2025 GMT
Mambobin kwamitin zartarwar na ADC da suka hada da Bolaji Abdullahi (Sakataren yada labarai na kasa), Babachir Lawal (Mataimakin shugaban jam’iyyar na yankin arewa maso gabas), Usani Uguru Usani (Mataimakin shugaban jam’iyyar na kasa), Farfesa Oserheimen Osunbor (Babban lauyan jam’iyyar na kasa), Bar Chinedu Idigbo (Sakataren shirye-shiryen jam’iyyar na kasa), Sen.
Duk da haka, INEC ba ta ki amincewa da sabbin shugabannin tare da kin saka sunayensu da hotunansu a shafinta na yanar gizo. Wannan lamari na ci gaban da damun mambobin jam’iyyar da magoya baya, yana nuna matsaloli a cikin jam’iyyar kafin 2027.
Sai dai yayin da yake mayar da martani ga wannan lamarin, sakataren yada labarai na jam’iyyar, Bolaji Abdullahi, ya shaida cewa INEC na bin ka’idojin aikinta ne, yana mai jaddada cewa za a warware rudanin a wannan makon.
Abdullahi, wanda ya kasance tsohon minista ya ce, “Abin da ke faruwa kawai shi ne bin ka’idoin aiki, hakika babu wani abu a ciki. Muna bukatar mu aika da wasu sa hannun kuma komi zai yi daidai.
“Jinkirin yana da alaka da ka’idojin gudanarwa ne kawai. Babu batun siyasah ko wani abu. Kawai yana da alaka ne da ka’idodin gudanarwa kuma za a shawo kan wannan lamari. Jinkirin yana da alaka da hanyoyin aiki kawai kuma zan iya gaya maka cewa a shawo kan lamarin a cikin wannan makon.”
Tun lokacin da aka kirkiri hadakar, shugabancin jam’iyyar yana ta samun suka tare da fadawa cikin rikice-rikice da ke tasowa a cikin jam’iyyar.
Masana sun cewa da tun lokacin da aka kafa kwamitin zatarwa karkashin jagorancin Mark, tsohon dan takarar shugaban kasa na ADC, Dumebi Kachikwu, ya kalubalanci kwamitin tare da bayyana Dabid Mark a matsayin shugaba na kawo rarrabuwar kai a jam’iyyar.
Yayin da yake tattaunawa da ‘yan jarida, Kachikwu ya zargi cewa an tilasta wa Mark zama shugaban wani bangare na ADC.
Kachikwu ya ce rashin adalci ne ga ‘yan Nijeriya a ce Atiku da Aregbesola da Mark su jagoranci hadakar jam’iyyar.
“Wannan wata barazana ce ga ‘yan Nijeriya da kuma mambobin jam’iyyar su kira Dabid Mark a matsayin shugaban jam’iyyar ADC. Ba shi ba ne shugaba. Ba zai iya zama ba. Mutanen da suka shigo jam’iyyar ta barauniyar hanya bai kamata su shugabanci jam’iyyarmu ba. Ba za mu kasa a gwiwa ba, duk da irin yakarmu da ake yi,” in ji shi.
Hazlika, tsohon dan takarar gwamna na ADC a Jihar Gombe, Nafiu Bala, ya bayyana cewa fatawar jam’iyyar a hannun Mark da Aregbesola ya saba wa dimokuradiyya kuma ya yi alkawarin yin gwagwarmaya a kan yakar lamarin.
Ya zargi Nwosu da sauran tsofaffin shugabannin jam’iyyar kan watsi da nauyin da aka dora musu kan tafiyar da harkokin jam’iiyyar kamar yadda tsarin mulki ya tanada.
Haka kuma Bala ya bayyana kansa a matsayin shugaban jam’iyyar ADC na wucin gadi tun da Nwosu ya yi murabus.
A yayin da yake mayar da martani ga wannan lamari, Nwosu ya shaida wace cewa rikicin shugabanci a jam’iyyar shiryayyan abu ne, yana zargin cewa akwai wadanda suke yin aiki ga fadar shugaban kasa, wanda yanzu suna cikin tashin hankali game da ADC.
“Zan ba da shawara ga ‘yan siyasa su mai da hankali kan bayar da ribar dimokuradiyya ga mutanensu, sannan su shirya don zabe mai zuwz maimakon lalata tsarin zabe ta haramtacciyar hanya,” in ji shi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: shugaban jam iyyar jam iyyar na kasa a jam iyyar
এছাড়াও পড়ুন:
Kotu ta tsige dan majalisar da ya sauya sheka zuwa APC
Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta tsige dan majalisar wakilai, Abubakar Gummi daga kujerarsa saboda sauya sheka daga jam’iyyar PDP zuwa APC.
Gummi yana wakiltar mazabar Gummi/Bukkuyum ta Jihar Zamfara a majalisar wakilai.
An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4m An sake kama shi a cikin ’yan fashi kwana 5 da fitowa daga kurkukuMai shari’a Obiora Egwuatu ne, ya yanke hukuncin, inda ya umarci kakakin majalisar wakilai, Tajudeen Abbas, da ya daina amincewa da Gummi a matsayin dan majalisar da ke wakiltar mazabar Gummi/Bukkuyum.
Haka kuma ya umarci hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) da ta shirya sabon zabe cikin kwanaki 30 domin cike gurbin kujerar dan majalisar.
Jam’iyyar PDP tare da shugaban ta na jihar Zamfara, Jamilu Jibomagayaki, ne suka shigar da karar dan majalisar.
Sun ce bai dace Gummi ya ci gaba da zama a kujerar ba bayan barin jam’iyyar da ta tsayar da shi takara.
Gummi, ta bakin lauyansa ya ce ya fice daga PDP ne saboda rikicin cikin gida da jam’iyyar ke fama da shi a matakin kasa da kuma a mazabarsa.
Amma kotu ta yi watsi da wannan hujjar, inda ta bayyana cewa babu takaddama da za ta ba shi damar ya sauya sheka.
A hukuncin da ya yanke, Mai shari’a Egwuatu ya ce ’yan siyasa dole su mutunta zabin jama’ar da suka kada musu kuri’a a karkashin jam’iyyar da ta tsayar da su takara.
Ya ce doka ba ta yadda da dan siyasa ya bar jam’iyyar da ta taimaka masa wajen lashe zabe sannan ya koma wata jam’iyya ba tare da ajiye mukaminsa ba.
Ya kara da cewa kuri’un da aka kada don dan takarar na jam’iyya ne, ba nasa ne na kashin kansa ba.
“Idan mutum yana son sauya sheka, ka da ya dauki amanar jama’ar da ta zabe shi ya tafi da ita,” in ji alkalin.
Kotu ta kuma umarci Gummi da ya daina karbar albashi da wasu hakkoki a matsayin dan majalisa, tare da mayar da duk kudaden da ya karba daga ranar 30 ga watan Oktoba, 2024, zuwa ranar da aka yanke hukuncin.
Haka kuma, ya gabatar da hujjar mayar da kudaden ga kotu cikin kwanaki 30.
Mai shari’a Egwuatu ya kuma ci Gummi tarar Naira N500,000, domin biyan PDP kudaden da ta kashe wajen shigar da kara.