Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC
Published: 6th, September 2025 GMT
Mambobin kwamitin zartarwar na ADC da suka hada da Bolaji Abdullahi (Sakataren yada labarai na kasa), Babachir Lawal (Mataimakin shugaban jam’iyyar na yankin arewa maso gabas), Usani Uguru Usani (Mataimakin shugaban jam’iyyar na kasa), Farfesa Oserheimen Osunbor (Babban lauyan jam’iyyar na kasa), Bar Chinedu Idigbo (Sakataren shirye-shiryen jam’iyyar na kasa), Sen.
Duk da haka, INEC ba ta ki amincewa da sabbin shugabannin tare da kin saka sunayensu da hotunansu a shafinta na yanar gizo. Wannan lamari na ci gaban da damun mambobin jam’iyyar da magoya baya, yana nuna matsaloli a cikin jam’iyyar kafin 2027.
Sai dai yayin da yake mayar da martani ga wannan lamarin, sakataren yada labarai na jam’iyyar, Bolaji Abdullahi, ya shaida cewa INEC na bin ka’idojin aikinta ne, yana mai jaddada cewa za a warware rudanin a wannan makon.
Abdullahi, wanda ya kasance tsohon minista ya ce, “Abin da ke faruwa kawai shi ne bin ka’idoin aiki, hakika babu wani abu a ciki. Muna bukatar mu aika da wasu sa hannun kuma komi zai yi daidai.
“Jinkirin yana da alaka da ka’idojin gudanarwa ne kawai. Babu batun siyasah ko wani abu. Kawai yana da alaka ne da ka’idodin gudanarwa kuma za a shawo kan wannan lamari. Jinkirin yana da alaka da hanyoyin aiki kawai kuma zan iya gaya maka cewa a shawo kan lamarin a cikin wannan makon.”
Tun lokacin da aka kirkiri hadakar, shugabancin jam’iyyar yana ta samun suka tare da fadawa cikin rikice-rikice da ke tasowa a cikin jam’iyyar.
Masana sun cewa da tun lokacin da aka kafa kwamitin zatarwa karkashin jagorancin Mark, tsohon dan takarar shugaban kasa na ADC, Dumebi Kachikwu, ya kalubalanci kwamitin tare da bayyana Dabid Mark a matsayin shugaba na kawo rarrabuwar kai a jam’iyyar.
Yayin da yake tattaunawa da ‘yan jarida, Kachikwu ya zargi cewa an tilasta wa Mark zama shugaban wani bangare na ADC.
Kachikwu ya ce rashin adalci ne ga ‘yan Nijeriya a ce Atiku da Aregbesola da Mark su jagoranci hadakar jam’iyyar.
“Wannan wata barazana ce ga ‘yan Nijeriya da kuma mambobin jam’iyyar su kira Dabid Mark a matsayin shugaban jam’iyyar ADC. Ba shi ba ne shugaba. Ba zai iya zama ba. Mutanen da suka shigo jam’iyyar ta barauniyar hanya bai kamata su shugabanci jam’iyyarmu ba. Ba za mu kasa a gwiwa ba, duk da irin yakarmu da ake yi,” in ji shi.
Hazlika, tsohon dan takarar gwamna na ADC a Jihar Gombe, Nafiu Bala, ya bayyana cewa fatawar jam’iyyar a hannun Mark da Aregbesola ya saba wa dimokuradiyya kuma ya yi alkawarin yin gwagwarmaya a kan yakar lamarin.
Ya zargi Nwosu da sauran tsofaffin shugabannin jam’iyyar kan watsi da nauyin da aka dora musu kan tafiyar da harkokin jam’iiyyar kamar yadda tsarin mulki ya tanada.
Haka kuma Bala ya bayyana kansa a matsayin shugaban jam’iyyar ADC na wucin gadi tun da Nwosu ya yi murabus.
A yayin da yake mayar da martani ga wannan lamari, Nwosu ya shaida wace cewa rikicin shugabanci a jam’iyyar shiryayyan abu ne, yana zargin cewa akwai wadanda suke yin aiki ga fadar shugaban kasa, wanda yanzu suna cikin tashin hankali game da ADC.
“Zan ba da shawara ga ‘yan siyasa su mai da hankali kan bayar da ribar dimokuradiyya ga mutanensu, sannan su shirya don zabe mai zuwz maimakon lalata tsarin zabe ta haramtacciyar hanya,” in ji shi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: shugaban jam iyyar jam iyyar na kasa a jam iyyar
এছাড়াও পড়ুন:
Taron Doha: Daga matakin Allawadai zuwa matakan kalubalantar laifukan Isra’ila
Babban daraktan kamfanin dillancin labaran kasar Qatar ya bayyana cewa taron gaggawa na kungiyar hadin kan kasashen musulmi ta OIC da ke tafe yana nuni da wani muhimmin sauyi na hadin kan kasashen larabawa da musulmi dangane da laifukan da ake aikatawa kan al’ummar Palastinu.
A cewar Pars Today, dukkanin idanuwa a ranakun Lahadi da Litinin (15-16 ga Satumba, 2025) za su kasance a Doha, babban birnin kasar Qatar, wanda zai karbi bakuncin taron gaggawa na shugabannin kasashen Larabawa da na Islama, don ba da amsa ga baki daya kan harin da Isra’ila ta kai kan Qatar.
Ana gudanar da wannan taron gaggawa ne a cikin yanayi na musamman na yanki da na duniya kuma ya biyo bayan harin da Isra’ila ta kai kan Qatar. Ana dai kallonsa a matsayin wani gagarumin sauyi ba wai kawai dangane da batun Falasdinu ba, har ma da sauran ci gaban siyasa a yankin.
A cikin wannan mahallin, masana da kwararru kan harkokin yada labarai na Qatar sun jaddada cewa zaluncin da Isra’ila ke yi wa Qatar ya farfado da ra’ayin kishin kasa na Larabawa tare da sake fasalin wasu muhimman batutuwan yankin.
Hadin kan Matsayin Larabawa da Musulunci
Ahmed Al-Rumaihi, Darakta-Janar na Kamfanin Dillancin Labarai na Qatar, ya ce hanyar shari’a ta kasa da kasa ita ce mafi kyawu kuma zabin da ya dace don tunkarar ci gaba da keta haddin ‘yan mamaya na (Sionist) – na farko daga cikin laifuffukan da aka rubuta da Benjamin Netanyahu, Firayim Ministan Isra’ila ya yi. Kotunan duniya, musamman kotun shari’a ta duniya, sun kafa sharuɗɗa da yawa waɗanda ke tabbatar da girman waɗannan laifuka.
Al-Rumaihi ya kara da cewa, ana ci gaba da yin Allah-wadai da wannan mugunyar ta’addancin da Isra’ila ke yi wa kasar Qatar, a duniya, kuma wannan ba wani abu ba ne, illa dai sakamakon yadda duniya ke kara wayar da kan jama’a game da keta haddin majalisar ministocin Isra’ila.
Farfado da Ra’ayin kishin Kasa
Babban editan jaridar Al-Sharq na kasar Qatar Jaber Al-Harami ya bayyana cewa, ha’incin da Isra’ila ta yi wa Qatar ya farfado da ra’ayin kishin kasa na Larabawa zuwa wani mataki da ba a taba ganin irinsa ba, wanda ke karfafa imanin cewa ba kasa daya ba ce kawai, yankin gaba daya. Al-Harami ya jaddada cewa, Isra’ila ba ta amince da wani jan layi ba, ba ta bi yarjejeniyoyin da aka kulla ko yarjejeniya ba, a maimakon haka tana aiwatar da munanan manufofin ba tare da la’akari da ka’ida ba.
A cewar Al-Harami, ta hanyar wannan wuce gona da iri Isra’ila na neman kafa sabbin sharudda da bukatu a karkashin shirin da ake kira “Isra’ila Babba”, inda ta sanya kasashen Larabawa a gaban wani zabi na wanzuwa. Don haka wajibi ne taron na Doha ya tashi daga kace-nace zuwa aiki na hakika.
Hakazalika, Nasser Al-Azba, wani lauya na kasa da kasa, ya jaddada cewa, lokaci ya yi da ya wuce yin Allah wadai da take-take, maimakon daukar matakai masu amfani da kuma daukar matakai masu inganci a kasa.
Al-Azba ya bayyana cewa, harin da Isra’ila ta kai kan Qatar a baya-bayan nan, ya nuna karara karya ce ga yarjejeniyar Vienna ta 1968, wadda ta kafa tsarin doka na kare jami’an diflomasiyya da masu shiga tsakani na kasa da kasa. A tarihi, manzanni sun kasance suna samun cikakkiyar kariya, kuma wannan ka’ida tana cikin dokokin duniya a yau.
Lauyan dokar kasa da kasa ya kara da cewa mayar da martani bai kamata ya takaita ga matakan shari’a ba, amma kuma dole ne ya hada da kulla kawance da kasashe da ba na yammacin Turai ba kamar su China, Rasha, da kasashen BRICS, yayin da a lokaci guda za a tattara ra’ayoyin jama’a na duniya don fallasa irin ta’addancin Isra’ila.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Ministan Tsaron Kasar venezuela Ya Gargadi Amurka Dangane Da Kokarin Juyin Mulki A Kasar September 16, 2025 Pezeshkian: Ya kamata kasashen musulmi su yanke alaka da gwamnatin sahyoniya September 16, 2025 Bayanin Bayan Taron Doha Ya Yi Kira Da A Kafa Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kare Kai September 15, 2025 Fira Ministan Spain: Bai Kamata A Rika Barin “Isr’ila” Tana Shiga Gasar September 15, 2025 Shugaban Kasar Iran Ya Gana Da Sarkin Kasar Qatar A Birnin Doha September 15, 2025 Dan Kasar Iran Mai Kirkira Ya Sami Kyautar Yabo A Kasar China September 15, 2025 Fizishkiyan: Wajibi Ne Musulmi Su Hada Kai Domin Dakatar Da Laifukan HKI September 15, 2025 Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Takwarorinsa Na Qatar, Turkiyya, Pakistan Da Labanon A Doha September 15, 2025 Kwamitin Kolin Tsron Kasar Iran Ya Amince Da Yarjejeniyar Da Aka Cimma Da Hukumar IAEA September 15, 2025 Jami’in Kasar Yemen Ya Aike Da Sako Ga Mahalarta Taron Birnin Doha Na Kasar Qatar September 15, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci