Muna Murna Da Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (1)
Published: 5th, September 2025 GMT
To Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wa Sallam, a matsayin aike shi ne karshe, shi ya zo da aike na karshe, wanda daga shi aiken Allah (Tabaraka Wa Ta’ala) ya kare. Sai dai na Manzon Allah (SAW) din nan ne za a yi ta bincikawa a yi ta gani saboda na Manzon Allah din nan yanzu ya dace da kowanne zamani. Ubangiji Tabaraka wa Ta’ala shi ne mai cikakken ilimi, shi ya halicci ilimi ma.
Galibin Annabawa kowa Allah yana aiko shi da iyakar ilimi da ya yi daidai da zamaninsa, duk idan muka duba a Alkur’ani za mu ga kowanne Annabi da irin kiran da ya yi. Cewar “a bauta ma Allah shi kadai” wannan na dukkan Annabawa ne, amma kuma za ka ga wani ya yi kira zuwa ga girmama iyaye, wani ya yi kira zuwa a yi awo da adalci, wani ya yi kira zuwa a yi tsarki, da sauransu, har aka zo kan Annabi Musa (AS) shine Mai Shari’a “Al-Kitabu”.
Allah ya ba Annabi Musa “Constitution” na abubuwa mai hukunce-hukunce wajen dari shida da wajen goma sha uku. Duk abinda Annabi Musa yake kai, da duk abin da zamaninsa yake kai sai da Allah ya rubuce masa shi a cikin Attaura. Kuma ya yi masa dalla-dallansa, sannan ya fitar da wadansu kyawawan dabi’u ya sanya masu suna “wasiyyoyi guda goma” (The Ten Commandments), su ma a cikin littafin suke amma saboda muhimmancin su ya sa Allah Tabaraka Wa Ta’ala ya ware su daban. Amma wannan sako na Attaura iya na wannan zamanin ne, iya na al’ummar Annabi Musa ne (Yahudu), ba zai zama har abada ba. Don haka da Annabi Isah (AS) ya zo sai ya gaya masu “to Ni kam Allah ya aiko Ni in saukaka wadannan hukunce-hukunce na Annabi Musa”. Kamar yanda shi ma Annabi Musa Allah ya saukaka masa ne daga hukunce-hukuncen Hamuraabi; wani sarki da aka yi a Babylon, kasar Iraki. Kila shi ma Annabi ne, kila Bawan Allah ne, amma dai Sarki ne kasaitacce wanda shi ya kafa dokoki masu yawa a cikin tsararensa na mulki (Constitution). Akwai kisa da yawa a cikin hukunce-hukuncensa, amma Allah sai ya sanya ma Annabi Musa kisa goma sha takwas kawai. Amma da Annabi Isah (AS) ya zo, shi kuma yanzu kiransa ba iyakar Bani Isra’ila (al’ummar Annabi Musa) kadai ba ne, Annabi Isah (AS) yana so ya fadada kiransa zuwa ga halitta baki daya, wanda kuwa yake son irin haka to dole hukunce-hukuncensa su zama masu sauki kuma masu kyau.
Ko su hukunce-hukuncen masu tsauri na Attaura da aka sanya ma Bani Isra’ila an sanya masu ne saboda zaluncinsu. Shi kuwa Annabi Isah (AS) da ya zo sai ya ce ma Bani Isra’ila ku yi imani da ni, ni kuwa zan dan saukaka maku wani abu daga cikin wadanda aka haramta maku. Akwai wani wa’azinsa da ya yi a majami’a (temple) da dare, ya ce masu: “a Attaura ta ce muku kaza ni kuwa na ce muku kaza, a Attaura ta ce kar ku ci kaza, ni kuwa na ce ku ci babu wani abu da zai shiga cikin Dan Adam da zai gurbata Dan Adam din nan, shi dan Adam maganarsa da take fitowa daga cikinsa da kuma mummunan kudirinsa su ne suke gurbata shi.
Don haka za ka ga mabiyan Annabi Isah ba su da wani abu na ci da yake haram, domin ya ce shi bai ga wani abu daga waje wanda zai shiga cikin Dan Adam ya gurbata shi ba, sai dai abin da yake cikin Dan Adam din ne kawai zai iya gurbata Dan Adam, ma’ana shi Dan Adam din ne najasar da kansa, domin daga cikinsa maganganun batancin suke fitowa. Sai Annabi Isah (AS) ya ce ma jama’arsa “amma kun ga Annabi Ahmadu (SAW) da zai zo, shi kuwa zai zubar muku da duk abubuwan da aka hana maku din nan gaba daya, zai zubar da duk wani kunci”. Amma idan mai tambaya ya tambaye ka to ya aka yi na ga Haram a cikin addinin Annabi Muhammad (SAW) masu tarin yawa? Amsar ita ce wannan duk aikin malamai da fakihai ne, su ne suka sanya mafi yawancin haramun din cikin addinin nan namu tun daga kan Sahabbai (Allah ya yarda da su) zuwa Tabi’ai zuwa abin da ya yi kasa, akwai su “Sadduz Zari’ati” akwai haramta duk wasu hanyoyi wadanda sai idan ka biyo ne sannan za su iya kai ka ga aikata laifin. To Alhamdu Lillahi, yanzu zamani ya kawo, ko ka zama Annabi Isah din; ka zubar da kadan, ko kuma ka zama al’ummar Annabi Muhammadu; ka zubar da gaba daya! Kur’aninka dai yana nan ya fada maka komai gaba daya.
Annabi Isah (AS) ya zo da abubuwa masu sauki, ya yada littafan da suka zo kafin sa, Allah ya sanya sauki a cikin lamarinsa, Allah ya sanya sauki a cikin mutanensa, don haka ‘Yan Adam suka karba, amma saboda sauki (domin duk abu in ya yi sauki to ya zama na ‘Yan Adam baki daya, haka kuma duk abu in ya yi tsauri to iya naku ne). Daga nan har Allah ya kawo Bulus, wanda almajirin Annabi Isah din ne, shi kuwa Bulus gaba daya ma sai ya watsar da dokokin Attaurar ma, sai ya dauki “wasayal ashri” din nan, kawai abin da ya dauka a cikin Attaura kenan. To mu ma ikon Allah, wannan “wasaya” guda goma Allah ya tafi da su a cikin Kur’aninmu, ita ce “Furkánu”.
To, amma idan muka zo wajen Annabi Muhammad (SAW) wanda shi ne karshen ma’aika, shi kuwa Allah Tabaraka Wa Ta’ala ya tattaro karatun fasahar “Engineering” din gaba daya ya damka masa (SAW). Duk littafin tafsirin da ka duba za ka ga ana yin sa ne daidai da wayewar al’ummar lokacin amma Alkur’anin kansa na farko ne na karshe ne, wata fahimtar ma tasa ba ta zo ba sai nan gaba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Tabaraka Wa Ta ala
এছাড়াও পড়ুন:
Burkina Faso: Masu Ikirarin Jihadi Sun Kashe Fararen Hula 50 A Cikin Watanni Hudu
Hukumar kare hakkin bil’adama ta “Human Right Watch” ta fitar da wani rahoto da a cikin ta bayyana cewa; kungiyar nan mai ikirarin jihadi a kasar Burkina Faso, ( Jama’at Nusratul-Islam wal Muslimin) da kuma kungiyar Daular Musulunci a cikin yankin Sahara, sun kashe fararen hula 50 daga watan Mayu zuwa yanzu.
Rahoton ya ci gaba da yin bayanin cewa, a cikin Ogusta kungiyoyin na masu riya cewa suna yin jihadi sun kashe mutane 40 a cikin garuruwan Djibo da Youba.
Rahoton ya kuma ce; a watan Yuli kuwa kungiyar IS ta kai wa fararen hula hari da suke kan hanyar kai kayan agaji zuwa garin Gorom-Gorom da aka killace da hakan ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 9.
Kungiyar kare hakkin bil’adama din ta ce, wadannan irin hare-haren sun sabawa dokokin kasa da kasa na jin kai, kuma suna a matsayin laifukan yaki.
Kungiyar kare hakkin bil’adaman ta “Human Right Watch” ta mika sakamakon binciken da ta gabatar ga hukumomin tsaro da na shari’a na kasar ta Burkina Faso. Sai dai har yanzu babu wani martani da ta samu.
Shekaru 3 kenan da kasar ta Burkan Faso take a karkashin mulkin soja da su ka sha alwashin kawo karshen masu tayar da kayar baya da sunan jihadi.
Tun daga 2016 ne kungiyoyin dake dauke da makamai suke kai hare-hare a sassa mabanbanta na kasar ta Burkina Faso da sunan jihadi.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Fira Ministan Spain: Bai Kamata A Rika Barin “Isr’ila” Tana Shiga Gasar September 15, 2025 Shugaban Kasar Iran Ya Gana Da Sarkin Kasar Qatar A Birnin Doha September 15, 2025 Dan Kasar Iran Mai Kirkira Ya Sami Kyautar Yabo A Kasar China September 15, 2025 Fizishkiyan: Wajibi Ne Musulmi Su Hada Kai Domin Dakatar Da Laifukan HKI September 15, 2025 Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Qatar, Turkiyya, Pakistan Da Labanon A Doha September 15, 2025 Kwamitin Kolin Tsron Kasar Iran Ya Amince Da Yarjejeniyar Da Aka Cimma Da Hukumar IAEA September 15, 2025 Jami’in Kasar Yemen Ya Aike Da Sako Ga Mahalarta Taron Birnin Doha Na Kasar Qatar September 15, 2025 Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada Sakamakon Kisan Kiyashin ‘Yan Sahayoniyya A Gaza Ya Kusaci 65,000 September 15, 2025 Gwamnatin Sudan Ta Ce: Babu Sulhu Da ‘Yan Tawayen Kasar Na Kungiyar Rapid Support Forces September 15, 2025 Kasashen Larabawa da na Musulmi na taron gaggawa kan harin Isra’ila a Qatar September 15, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci