Aminiya:
2025-09-18@00:43:25 GMT

Cin amana shi ne tsarin siyasa a Najeriya — Jonathan

Published: 5th, September 2025 GMT

Tsohon Shugaban Ƙasa, Goodluck Jonathan, ya ce siyasar Nijeriya ta ginu ne a kan cin amana, la’akari da irin cin amanar da ya ce ya fuskanta matuƙa a lokacin da yake neman tazarce a Zaben 2015.

Jonathan ya bayyana haka ne a wurin bikin cika shekara 70 na tsohon abokinsa, Cif Mike Aiyegbeni Oghiadomhe, da aka gudanar a Benin, babban birnin Jihar Edo, a ranar Alhamis.

An naɗa Benjamin Hundeyin sabon kakakin ’yan sandan Nijeriya Ɓarkewar cutar Ebola ta kashe mutum 15 a Congo

Ya ce daga cikin abubuwan da ya fahimta a siyasar Najeriya shi ne wahalar samun ɗan siyasa mai gaskiya da tsayawa a kan kalamansa.

A cewarsa, galibin ’yan siyasar Nijeriya ba su da riƙon gaskiya ko amana, sai dai ya yaba da Oghiadomhe a matsayin mutumin da ya fita daban cikin ’yan siyasar ƙasar.

“A halin yanzu siyasar Nijeriya ta ta’allaƙa ne da cin amana. Saboda zai yi wuya ka samu ɗan siyasar da zai faɗi wani abu ɗaya da safe, ya tsaya a kai har zuwa rana ko zuwa yamma.

“A cikin ’yan mintuna kaɗan za su faɗi abu ɗaya, amma bayan awa guda sai su sauya magana,” in ji Jonathan.

Sai dai ya bayyana cewa Cif Oghiadomhe na daga cikin ’yan siyasa ƙalilan da zai iya sadaukar da rayuwarsa saboda shi.

“A wurina, Oghiadomhe mutum ne da za a iya kai kalamansa banki a ajiye, saboda gaskiyarsa da amana. Amma yawancin ’yan siyasa kuwa, ba za ka iya dogaro da kalamansu ba,” in ji shi.

Ana iya tuna cewa, Cif Oghiadomhe ne ya yi wa Jonthan Shugaban Ma’aikata na Fadar Shugaban Ƙasa daga 2010 zuwa 2014, wanda tsohon shugaban ya nanata jin daɗin alaƙarsa da shi.

Daga cikin manyan baƙin da suka halarci taron akwai tsohon shugaban APC na ƙasa, Sanata Adams Oshiomhole, tsofaffin gwamnonin Edo, Lucky Igbinedion da Oserheimen Osunbor, tsohon Gwamnan Gombe Ibrahim Hassan Dankwambo, tsohon Shugaban Ma’aikata na Fadar Gwamnatin Edo, Farfesa Izia Ize-Iyamu da sauran jiga-jigai.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Zaɓen 2015

এছাড়াও পড়ুন:

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

Hukumar NDLEA ta bayyana cewa wata ƙungiyar masu safarar miyagun ƙwayoyi ce a filin jirgin sama na Kano ta boye jakunkunan ƙwayoyi a cikin kayan matafiyan.

An kama shugaban ƙungiyar, Ali Abubakar Mohammed (wanda aka fi sani da Bello Karama), tare da wasu abokan aikinsa.

Hukumar ta ce mutanen ukun ba su da laifi kuma an zalunce su ne kawai.

An saki su ne bayan bincike da kuma ƙoƙarin diflomasiyya na tsawon makonni.

Lamarin ya tayar da hankali kan tsaro a filayen jirgin sama a Nijeriya da yadda masu aikata laifuka ke amfani da fasinjoji marasa laifi.

Hukumar ta ce za a ɗauki ƙarin matakai don hana faruwar irin wannan lamari.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu
  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Sabon Tsarin Kula Da Lafiyar Mata Masu Juna Biyu Da Kananan Yara
  • Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
  • Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana
  • NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba
  • Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa
  • An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya
  • Peter Obi ya kai wa Obasanjo ziyara
  • An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar