Cin amana shi ne tsarin siyasa a Najeriya — Jonathan
Published: 5th, September 2025 GMT
Tsohon Shugaban Ƙasa, Goodluck Jonathan, ya ce siyasar Nijeriya ta ginu ne a kan cin amana, la’akari da irin cin amanar da ya ce ya fuskanta matuƙa a lokacin da yake neman tazarce a Zaben 2015.
Jonathan ya bayyana haka ne a wurin bikin cika shekara 70 na tsohon abokinsa, Cif Mike Aiyegbeni Oghiadomhe, da aka gudanar a Benin, babban birnin Jihar Edo, a ranar Alhamis.
Ya ce daga cikin abubuwan da ya fahimta a siyasar Najeriya shi ne wahalar samun ɗan siyasa mai gaskiya da tsayawa a kan kalamansa.
A cewarsa, galibin ’yan siyasar Nijeriya ba su da riƙon gaskiya ko amana, sai dai ya yaba da Oghiadomhe a matsayin mutumin da ya fita daban cikin ’yan siyasar ƙasar.
“A halin yanzu siyasar Nijeriya ta ta’allaƙa ne da cin amana. Saboda zai yi wuya ka samu ɗan siyasar da zai faɗi wani abu ɗaya da safe, ya tsaya a kai har zuwa rana ko zuwa yamma.
“A cikin ’yan mintuna kaɗan za su faɗi abu ɗaya, amma bayan awa guda sai su sauya magana,” in ji Jonathan.
Sai dai ya bayyana cewa Cif Oghiadomhe na daga cikin ’yan siyasa ƙalilan da zai iya sadaukar da rayuwarsa saboda shi.
“A wurina, Oghiadomhe mutum ne da za a iya kai kalamansa banki a ajiye, saboda gaskiyarsa da amana. Amma yawancin ’yan siyasa kuwa, ba za ka iya dogaro da kalamansu ba,” in ji shi.
Ana iya tuna cewa, Cif Oghiadomhe ne ya yi wa Jonthan Shugaban Ma’aikata na Fadar Shugaban Ƙasa daga 2010 zuwa 2014, wanda tsohon shugaban ya nanata jin daɗin alaƙarsa da shi.
Daga cikin manyan baƙin da suka halarci taron akwai tsohon shugaban APC na ƙasa, Sanata Adams Oshiomhole, tsofaffin gwamnonin Edo, Lucky Igbinedion da Oserheimen Osunbor, tsohon Gwamnan Gombe Ibrahim Hassan Dankwambo, tsohon Shugaban Ma’aikata na Fadar Gwamnatin Edo, Farfesa Izia Ize-Iyamu da sauran jiga-jigai.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Zaɓen 2015
এছাড়াও পড়ুন:
Muna shirin kai farmaki a Nijeriya — Ma’aikatar Yaƙin Amurka
A yayin da ake ci gaba da cece-kuce kan kalaman Shugaban Amurka Donald Trump da ke zargin gwamnatin Nijeriya da watsi da batun kisan Kiristoci a ƙasar, Ma’aikatar Yaƙin Amurka ta bayyana cewa ta fara shirin kai farmaki a Nijeriya.
Sakataren Ma’aikatar, Pete Hegseth, ne ya tabbatar da hakan cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X a ranar Asabar, yana mai cewa ma’aikatarsa “na shirye-shiryen ɗaukar mataki” bayan umarnin da Trump ya bayar.
Jamus ta shiga sahun ƙasashen da ke neman kawo ƙarshen yaƙin Sudan Tinubu zai gana da Trump kan zargin kisan Kiristoci a Nijeriya“Muna shirye-shirye don ɗaukar mataki a Nijeriya. Idan gwamnatin Nijeriya ba ta kare Kiristoci ba, za mu kai hari, mu kawar da ‘yan ta’addan Musulmai da ke aikata wannan ta’asar,” in ji Hegseth.
Trump dai ya yi wannan barazanar ne a cikin wani saƙo da ya wallafa a Truth Social, inda ya ce Amurka za ta dakatar da duk tallafin da take bai wa Nijeriya, kuma tana iya “shiga ƙasar da ƙarfin soji domin share ‘yan ta’addan da ke kashe Kiristoci.”
“Idan gwamnatin Nijeriya ta ci gaba da bari ana kashe Kiristoci, Amurka za ta dakatar da duk wata tallafi, kuma mai yiwuwa ta shiga wannan ƙasar, ta cike da ƙarfin gwiwa domin kawar da ’yan ta’addan Musulmai masu zafin kishin addini,” in ji Trump.
Ya kuma gargaɗi gwamnatin Nijeriya da ta gaggauta ɗaukar mataki, yana cewa idan Amurka ta kai farmaki “za ta yi shi cikin sauri, da tsananin ƙarfi, da gamsuwa.”
Lamarin na zuwa ne kwana guda bayan Trump ya mayar da Nijeriya cikin jerin ƙasashen da za a sanyawa ido, yana zargin cewa “ana yi wa Kiristoci kisan gilla” a hannun ƙungiyoyin Musulmi masu tsattsauran ra’ayi.
Sai dai a martanin da ya mayar, Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya ce Nijeriya tana nan daram a matsayin ƙasa mai dimokuraɗiyya wadda kundin tsarin mulkinta ke tabbatar da ‘yancin yin addini da haƙuri tsakanin mabambantan addinai.
“Tun daga shekarar 2023, gwamnatinmu tana gudanar da tattaunawa sosai da shugabannin addinai na Kiristanci da Musulunci, tare da ci gaba da magance matsalolin tsaro da ke shafar ‘yan ƙasa daga addinai da yankuna daban-daban,” in ji Tinubu.
A cewar mai ba wa Tinubun shawara na musamman kan yaɗa manufofi, Daniel Bwala, za a yi ganawa tsakanin Shugaba Tinubu da Shugaba Trump “a cikin kwanaki kaɗan masu zuwa” domin tattaunawa da warware wannan saɓanin fahimta.