Aminiya:
2025-09-17@21:47:25 GMT

Saudiyya ta ƙaƙaba wa masu laifukan rashin ɗa’a sabuwar tara

Published: 5th, September 2025 GMT

Gwamnatin Saudiyya ta sanar da sanya tarar kuɗi kan masu aikata ayyukan da suka shafi rashin ɗa’a a cikin al’umma, musamman a lokutan salla, domin kare mutunci, tsaro da kuma zaman lafiya.

Sabbin matakan, wanda za a fara aiwatarwa nan take, sun shafi masu sanya kaya marasa mutunci a bainar jama’a, da masu kunna kiɗa lokacin salla, da masu bahaya ko zubar da shara a wuraren da doka ta haramta.

Sojoji sun kashe ’yan Boko Haram 13 a Borno Hisbah ta kama mai safarar mutane da mata 12

A cewar sabuwar doka, duk wanda aka kama da kunna kiɗa a lokacin salla zai biya tara ta Riyal 1,000 (kimanin Naira 390,000) a karon farko, kuma idan aka sake kama shi, tarar za ta ninka zuwa Riyal 2,000 (kimanin Naira 780,000).

Haka kuma, duk wanda ya sa tufafi marasa mutunci a bainar jama’a za a ci shi tara ta Riyal 100, sannan idan ya sake maimaitawa tarar za ta ƙaru zuwa Riyal 500.

An kuma haramta zubar da shara ko bahaya a wuraren da doka ta hana. Kuma duk wanda ya karya wannan doka a karon farko zai biya Riyal 500, sannan a karo na biyu tarar za ta ninka zuwa Riyal 1,000.

Bugu da ƙari, duk wanda aka kama yana ɗaukar hoto ko bidiyo ba tare da izini ba, za a ci shi tara ta Riyal 1,000, sannan idan ya maimaita laifin tarar za ta ninka zuwa Riyal 2,000.

Sabbin dokokin na Saudiyya na zuwa ne a daidai lokacin da gwamnati ke ƙoƙarin ƙara tsaurara matakan ladabtar da jama’a, musamman a wuraren ibada da jama’ar musulmi ke taruwa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Rashin ɗa a Saudiyya Tara tarar za ta

এছাড়াও পড়ুন:

DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Doya A Wasu Kasuwannin Najeriya

A daidaikun kasuwannin Abuja da wasu manyan birane na ƙasar nan, an bayyana yadda farashin doya ke ƙara hawa fiye da yadda ake tsammani.

 

Wannan na faruwa ne duk da cewa yanzu sabuwar doya ta fara shigowa kasuwa, bisa al’ada, a duk shekara fitowar sabuwar doya kan karya farashin wanda yake kasuwa. Sai dai a bana, wasu daililai na sa farashin doya kara hawa.

NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba DAGA LARABA: Dalilan Da Suka Sa Nayi Yunkurin Kashe Kaina Har Sau Uku

wannan shine batun da shirin Daga Laraba na wannan makon zai yi duba akai.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Saudiyya ta saki ’yan Najeriya 3 da ta kama kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi
  • ‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Ta Kama Bisa Kuskuren Safarar Ƙwayoyi
  • Tun Tinubu yana Gwamna ba abin da ya fi shahara da shi kamar tara haraji – Adebayo
  • DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Doya A Wasu Kasuwannin Najeriya
  • NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba
  • Taron Doha: Daga matakin Allawadai zuwa matakan kalubalantar laifukan Isra’ila
  • Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar
  • An kama mabaraci da kuɗaɗen ƙasar waje a Ilorin