Aminiya:
2025-11-02@06:24:53 GMT

Saudiyya ta ƙaƙaba wa masu laifukan rashin ɗa’a sabuwar tara

Published: 5th, September 2025 GMT

Gwamnatin Saudiyya ta sanar da sanya tarar kuɗi kan masu aikata ayyukan da suka shafi rashin ɗa’a a cikin al’umma, musamman a lokutan salla, domin kare mutunci, tsaro da kuma zaman lafiya.

Sabbin matakan, wanda za a fara aiwatarwa nan take, sun shafi masu sanya kaya marasa mutunci a bainar jama’a, da masu kunna kiɗa lokacin salla, da masu bahaya ko zubar da shara a wuraren da doka ta haramta.

Sojoji sun kashe ’yan Boko Haram 13 a Borno Hisbah ta kama mai safarar mutane da mata 12

A cewar sabuwar doka, duk wanda aka kama da kunna kiɗa a lokacin salla zai biya tara ta Riyal 1,000 (kimanin Naira 390,000) a karon farko, kuma idan aka sake kama shi, tarar za ta ninka zuwa Riyal 2,000 (kimanin Naira 780,000).

Haka kuma, duk wanda ya sa tufafi marasa mutunci a bainar jama’a za a ci shi tara ta Riyal 100, sannan idan ya sake maimaitawa tarar za ta ƙaru zuwa Riyal 500.

An kuma haramta zubar da shara ko bahaya a wuraren da doka ta hana. Kuma duk wanda ya karya wannan doka a karon farko zai biya Riyal 500, sannan a karo na biyu tarar za ta ninka zuwa Riyal 1,000.

Bugu da ƙari, duk wanda aka kama yana ɗaukar hoto ko bidiyo ba tare da izini ba, za a ci shi tara ta Riyal 1,000, sannan idan ya maimaita laifin tarar za ta ninka zuwa Riyal 2,000.

Sabbin dokokin na Saudiyya na zuwa ne a daidai lokacin da gwamnati ke ƙoƙarin ƙara tsaurara matakan ladabtar da jama’a, musamman a wuraren ibada da jama’ar musulmi ke taruwa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Rashin ɗa a Saudiyya Tara tarar za ta

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji Sun Ceto Wani Mutum Da Aka Sace A Taraba

Ana zargin mutumin da hannu wajen sace Alhaji Adamu.

Wanda ake zargin ya samu raunuka bayan jama’a sun yi masa duka kafin isowar sojoji, kuma an garzaya da shi asibiti, yayin da ake ci gaba da bincike.

Brigedi Janar Kingsley Chidiebere Uwa, kwamandan Rundunar 6, ya yaba da yadda sojoji, ‘yan sa-kai da mafarauta suka haɗa kai, yana mai cewa wannan haɗin kai ya taimaka wajen samun nasarar ceto wanda aka sace.

Ya kuma buƙaci jama’ar Taraba su ci gaba da bai wa hukumomin tsaro sahihan bayanai da wuri domin tabbatar da zaman lafiya da tsaro a faɗin jihar.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai Majalisar Dokokin Kano Ta Ce An Yi Rashin Adalci Wajen Ɗaukar Aikin Kwastam A Nijeriya October 30, 2025 Manyan Labarai Bai Kamata Gwamnati Ta Ke Ciyo Bashi Bayan Cire Tallafin Man Fetur Ba – Sanusi II October 30, 2025 Manyan Labarai Atiku Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Sauya Sunayen Waɗanda Aka Yi Wa Afuwa October 30, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa
  • Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai
  • Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa
  • Matsalar Talauci Da Rashin Tsawon Rai Da ‘Yan Nijeriya Ke Fuskanta
  • An sake kama shi a cikin ’yan fashi kwana 5 da fitowa daga kurkuku
  • Madagascar Ta Sanar da Kafa Sabuwar Gwamnati Tare da Manyan ‘Yan Adawa
  • Ana zargin ɗa da kashe mahaifinsa a Kano saboda hana shi ƙara aure
  • Gwamnatin Gombe ta saurari ra’ayoyin jama’a kan kasafin kuɗin 2026
  • Sojoji Sun Ceto Wani Mutum Da Aka Sace A Taraba
  • Majalisar Dokokin Kano Ta Ce An Yi Rashin Adalci Wajen Ɗaukar Aikin Kwastam A Nijeriya