Kwankwaso zai iya komawa APC – Abdulmumin Kofa
Published: 4th, September 2025 GMT
Hon Abdulmumin Jibrin Kofa, dan Majalisar Wakilan Najeriya ya ce jagoran jam’iyyar NNPP na kasa, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso a shirye yake ya tattauna da jam’iyyar APC kan batun komawa cikinta.
Dan majalisar, wanda makusancin Kwankwason ne dai a ’yan makonnin da suka gabata sau biyu yana ganawa da Shugaban Kasa Bola Tinubu a fadarsa da ke Abuja a kan batun Kwankwason.
Kofa ya bayyana hakan ne yayin tattaunawarsa da gidan talabijin na Channels a shirinsu mai suna Politics Today ranar Laraba.
Sai dai Kofa wanda ke wakiltar mazabar Kiru/Bebeji a majalisar ya ce ya ce wasu daga cikin ’yan jam’iyyar ta APC a jiharsu ta Kano ba za su so komawar tsohon Gwamnan na Kano ba.
Amma ya ce har yanzu ana ci gaba da tattaunawa a kan batun.
Ya ce, “Idan ka ce Kwankwaso zai koma APC, ko kuma za mu koma APC, hatta a cikin ita APC din a Kano, akwai mutane da yawa da ba za su so ya koma ba, watakila masu son zama Gwamna da ma wadanda ba Gwamnan suke son zama ba.
“Na yi iya kokarina wajen ganin siyasar Kano da ta Najeriya ta daidaita, amma tana da sarkakiya sosai.
“Amma kowa ya sani, tun daga farkon wannan gwamnatin, na yi ta fadi-tashin ganin mun yi aiki tare wajen kafa gwamnatin hadin kan kasa.
“In dai maganar komawa APC ce, ya sha nanata cewa kofarsa ta tattaunawa a bude take, kofofinmu a bude suke, komai zai iya faruwa,” in ji dan Majalisar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Kwankwaso
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Kano Ta Inganta Cibiyoyin Horas Da Sana’o’i Domin Dakile Aikata Laifuka Tsakanin Matasa
Gwamnatin Kano ta raba kayayyakin aiki na zamani na kimanin Naira Miliyan 250 ga cibiyoyin horas da sana’o’in hannu biyu da ke Kofar Mata da Gwale, domin yaƙi da shan miyagun kwayoyi da aikata laifuffuka a tsakanin matasa, ta hanyar samar da aikin yi.
Kwamishinan Kimiyya da Fasaha, Dakta Yusuf Kofarmata, ya ce an amince da tallafin ne bisa umarnin Gwamna Abba Kabir Yusuf don bunƙasa tsare-tsaren ƙarfafa matasa a jihar.
Ya bayyana cewa an samar da injinan sarrafa fata guda 26 domin cibiyoyin wadanda al’ummar yankunan suka kafa, amma ba su da isassun kayayyakin aiki.
Ya ce Gwamna Yusuf ne ya gina Cibiyar Horaswar ta Gwale kasancewar nan ce mazabarsa, yayin da Dakta Yakubu Adam ya taka rawa wajen gina ta Kofar-Mata.
Ya ce cibiyoyin za su samar da daruruwan ayyukan yi tare da rage matsalolin zaman kashe-wando da ta’addanci a tsakanin matasa.
A nasa jawabin, Ali Musa Kofar-Mata na ƙungiyar IKMA ya gode wa gwamnati bisa wannan gudummawar da ya kira mai sauya rayuwa.
Ya ce cibiyar ta fara ɗaukar matasa maza da mata, kuma horon zai ɗauki watanni uku kafin a shiga sabon zagaye.
Abdullahi Jalaluddeen