Kwankwaso zai iya komawa APC – Abdulmumin Kofa
Published: 4th, September 2025 GMT
Hon Abdulmumin Jibrin Kofa, dan Majalisar Wakilan Najeriya ya ce jagoran jam’iyyar NNPP na kasa, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso a shirye yake ya tattauna da jam’iyyar APC kan batun komawa cikinta.
Dan majalisar, wanda makusancin Kwankwason ne dai a ’yan makonnin da suka gabata sau biyu yana ganawa da Shugaban Kasa Bola Tinubu a fadarsa da ke Abuja a kan batun Kwankwason.
Kofa ya bayyana hakan ne yayin tattaunawarsa da gidan talabijin na Channels a shirinsu mai suna Politics Today ranar Laraba.
Sai dai Kofa wanda ke wakiltar mazabar Kiru/Bebeji a majalisar ya ce ya ce wasu daga cikin ’yan jam’iyyar ta APC a jiharsu ta Kano ba za su so komawar tsohon Gwamnan na Kano ba.
Amma ya ce har yanzu ana ci gaba da tattaunawa a kan batun.
Ya ce, “Idan ka ce Kwankwaso zai koma APC, ko kuma za mu koma APC, hatta a cikin ita APC din a Kano, akwai mutane da yawa da ba za su so ya koma ba, watakila masu son zama Gwamna da ma wadanda ba Gwamnan suke son zama ba.
“Na yi iya kokarina wajen ganin siyasar Kano da ta Najeriya ta daidaita, amma tana da sarkakiya sosai.
“Amma kowa ya sani, tun daga farkon wannan gwamnatin, na yi ta fadi-tashin ganin mun yi aiki tare wajen kafa gwamnatin hadin kan kasa.
“In dai maganar komawa APC ce, ya sha nanata cewa kofarsa ta tattaunawa a bude take, kofofinmu a bude suke, komai zai iya faruwa,” in ji dan Majalisar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Kwankwaso
এছাড়াও পড়ুন:
PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu da ke da alaƙa da Wike
Rikici a babbar jam’iyyar adawa ta PDP, na ƙara ƙamari, bayan da jam’iyyar ta dakatar da sakatarenta na ƙasa, Sanata Samuel Anyanwu, da wasu da ake ganin ’yan tsagin Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike ne.
Mai magana da yawun jam’iyyar na ƙasa, Debo Ologunagba ne, ya sanar da dakatarwar bayan wani taro da Kwamitin Ayyuka na Ƙasa (NWC), ya gudanar a hedikwatar jam’iyyar da ke Abuja.
Zargin Kisan Kiristoci: Maganar Trump a kan Najeriya tsagwaron ƙarya ce — Shehu Sani Zaɓen Tanzania: Shugaba Samia ta yi tazarce da kashi 97 an ƙuri’uSauran da aka dakatar sun haɗa da Mai Bai wa jam’iyyar Shawara kan Harkokin Shari’a, Kamaldeen Ajibade (SAN); Sakataren Tsara Harkokin Jam’iyya, Umar Bature; da Mataimakin Mai Bai wa jam’iyyar Shawara kan Harkokin Shari’a.
Rahotanni sun bayyana cewa waɗanda aka dakatar ba sa halartar tarukan jam’iyyar.
An dakatar da su na tsawon wata ɗaya, sannan aka miƙa lamarinsu ga Kwamitin Ladabtarwa na jam’iyyar PDP domin gudanar da bincike.
Waɗanda aka dakatar ’yan tsagin Wike ne, kuma sun raba ƙafa a rikicin da jam’iyyar ke fuskanta tun bayan zaɓen 2023.
Idan ba a manta ba, a ranar Juma’a ne, wata Babbar Kotu a Babban Birnin Tarayya, ta dakatar da PDP daga shirin gudanar da babban taronta da aka tsara yi a Ibadan, Jihar Oyo, a ranar 15 da 16 ga watan Nuwamba, 2025.
Sai dai jam’iyyar ta ce za ta ɗaukaka ƙara kan hukuncin, kuma hakan ba zai hana ta ci gaba da shirye-shiryen gudanar da taron ba.
Wasu daga cikin ’ya’yan jam’iyyar sun ce rashin jituwa a PDO shi ne babban dalilin da ya sa aka kai ƙarar taron’ kotu.